ADS HERE
Posts

JANNAT (tsugunno bata ƙare ba) page 3

 *⚖️👩‍🎓🎓 JANNAT (tsugunno bata kare ba)🎓👩‍🎓⚖️*


_LABARI DA RUBUTAWA (MRS ABDULL CE✍️)_


*Hakkin mallaka na mrs Abdull ne kawai ban yarda wani ko wata ya juya min labari na ta kowacce siga ba hakan laifi ne mai girma kuma tabbas zan dau mataki, idan suna ko halayya yazo daya akasi ne, labari na kirkirarren labari ne banyi shi dan cin zarafi ko tozarci ga wani ko wata ba, kuma insha Allah zan ringa posting sau hudu ne a sati*



_Littafin SADAUKARWA ne ga mamana *Khadijah sulaiman Gombe* alkairan Allah su tadda ki har gadon bacci_


https://chat.whatsapp.com/JWinbPSk9h5FGL7KmFbWg1

 *_________________________________*


 *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*

*🇦SSOCIATION🤝🏻*

 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_________________________________*



*Kasan addinin ka*


```LOKUTA HUDU NA AMSA ADDU'A```


           Da Sunan Allah Mai Rahma Mai Jin ƙai


3. RANAR JUMA'A BAYAN LA'SAR: Haka Kuma Bayan Sallar La'asar Na Ranar Juma'a Kamar Yanda Mafi Yawan Malamai Suka Rinjayar Lokaci ne da Ubangiji Yake Amsa Addu'ar Bayi. Manzon Allah (ﷺ) Yana Cewa:


ﻋَﻦ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ رَضِي اللَّهُ عَنهُ، ﺃَﻥَّ ﺭَﺳُﻮﻝَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﷺ ﺫَﻛَﺮَ ﻳَﻮْﻡَ ﺍﻟﺠُﻤُﻌَﺔِ، ﻓَﻘَﺎﻝَ : ‏”ﻓِﻴﻪ ﺳَﺎﻋَﺔٌ ﻻ ﻳُﻮَﺍﻓِﻘﻬﺎ ﻋَﺒْﺪٌ ﻣُﺴﻠِﻢٌ، ﻭَﻫُﻮ ﻗَﺎﺋِﻢٌ ﻳُﺼَﻠِّﻲ ﻳﺴﺄَﻝُ ﺍﻟﻠَّﻪ ﺷَﻴْﺌًﺎ، ﺇِﻻَّ ﺃَﻋْﻄَﺎﻩُ ﺇِﻳَّﺎﻩ“

{البخاري: ٩٣٥}


An Kar6o Daga Abi-Hurairah (ra), Lallai Annabi (ﷺ) Ya Ambaci Ranar Juma'a Sai Yace: “A Cikinta Akwai Wani Lokacin da Babu Bawa Musulmi da Zai Dace Dashi, Ya Tashi Yayi Sallah, Sannan Ya Roqi Allah Wani Abu, Face Allah Ya Bashi Wannan Abin”.

{Bukhari: 935}



______________________________📲


~SHAFI NA UKU~



Washe gari haka JANNAT ta tashi kamar babu wani abinda ya faru jiya, domin a ganin ta nuwairah bata isa ta daura mata  hawan jini ba! Kasancewar asabar ya saka basu tashi da wuri ba, sai wajen 8 sannan ta tashi tun bayan da ta koma sallan asuba, kicin ta shiga ta fara ayki sannan ta dawo ta tashi su nasmah da nasreen, duk kudin da suke dashi baya hana wa ta saka su su tiƙi aiki duk da kananun shekarun su kuwa, ko wanke banɗaki ta saka su tas suke wanke wa ya fita, dan haka ta taso su, break fast tayi masu mai ma'ana da kama hankali babu wani tarkace, abinci mai kama ciki ta jera a dining da su ruwan zafi da kayan tea sannan suka tafi yin wanka, sai da suka kammala, sannan suka fito , HUDAY da juniour har sun fito su suke jira dan haka su nasmah suka gaida su sannan suka hau dining. (JANNAT Bata wasa wajen koya wa yara tarbiyya, ko kadan dole na sama ya ji tausayin na kasa shi kuma na kasa ya girmama babba haka take goyon ta bata yadda da raini ko rashin tausayi ba a tsarin ya) 

Bayan sun gama cin abinci kuma aka shiga kimtsa gida, zaka ji mamakin yanda nasreen ta zage take wanke toilet din dakin juniour daga jikin bango har ƙasa haka ta ringa tiƙar ayki,ita kuma nasmah nasu take wanke wa ,uwar gayyar kuwa na mijin ta, juniour ba'a barshi a baya ba, kayan kicin yake ta gyara wa,mai gidan kuma takaddun su duka nashi da na uwar da na yaran, haka suke kasancewa duk karshen mako cikin wannan gyare-gyaren, tsarinsu yana da matukar burgewa da bada abin sha'awa.

Tass suka gama zuwa karfe 1 na rana gida ya dauki sanyi da kamshi ko ina kyalli yake, gwanin ban sha'awa, Kasancewar aykin da suka yi mai wahala,sai ta ɗora musu abinci mai sauki duk suka shiga wanka, zuwa biyu kowa ya hallara a parlou,sun fito cin abinci kenan sai ga kiran waya, amma a wayar gida dan haka nasmah taje ta dauka, cikin wayar taji an ce ''ma'am AKWAI baƙi a waje'', cikin Muryar ta mai sanyi na mara sa son magana tace, ''ammi akwai baƙi.'' ta fada da karfi yanda JANNAT da ke kan dining zata ji! Ki tanbaya su wanene, JANNAT ta fada itama. '' Yaya Ishaq su wanene inji ammi?''(yana daga cikin tarbiyyar JANNAT dole ka kira na sama da kai yaya dan haka hatta polisawa da suke masu gadi da kaisu makaranta da yaya suke kiransu,sabanin wani gidan masu kudin da za'a ke walaƙanta masu ayki.)

Daga cikin wayar aka ce ''way sadiya kaltanga ce.''

Ihun murna nasmah ta saka tana fadin ''kace ta shigo yaya Ishaq'' shima daga can dariya yayi don ya san sadiya bazama ayi mata ka'idar shiga ba yau ne day kawai ta nemi yayi hakan dan haka yayi kuma Allah shi ya barwa kansa sanin mai yasa ta fadi hakan. Cikin dariya Ishaq yace ''ok ma'am.'' 

'bata fuska nasmah tayi ta tsani Ishaq ya ringa fadi mata ma'am dinnan Amma yaki bari, ''ni ba ma'am bace ta fada tana datse wayar, dariya ya kwashe dashi ya rasa dalilin da ya saka nasmah ke burgeshi ''yarinya yar 11 Yes sai shiga rai'' ya fada cikin ranshi sannan ya juya yace ranki ya dade zaki iya shiga, horn ta sake yi dan haka aka bude mata makeken gate din ta cusa kan motar cikin gidan.

A cikin parlou kuwa HUDAY ne yace kai! ''Kai!! Kai!!! Nasmah lafiyan ki kam day ko? Menene?''

Cikin dariya tace '' Abba way anty sadiya kaltanga ita tazo shine fa take tanbayar IZININ shigowa kasan anty sadiya ay'' ta fada tana dariya.

Kafin ya ce komai sai gashi an turo kofar parloun ana fadin surprise! surprise! Dukan su dariya suka saka har HUDAY don sadiya ba dai shakiyanci ba ta iya shi yanki yanki, 

Harara JANNAT ta watsa mata sannan ''tace shine harda saka Ishaq ya kira ko?''

''eh mana na yiwa ƴaƴa na bazata ba kuma gashi ya sunji dadin zuwa na idan ke Baki ji dadi ba'' itama wacce suke kira sadiya ta faɗa tana neman guri ta zauna, kamar su daya da JANNAT daga kallo daya zaka fahimci jini ɗaya ne su uwa daya uba daya sabida tsananin kama da suke yi. 

''Ko Ni naji daɗi dan yau gidan akwai cin dariya,'' HUDAY ya faɗa yana gyara zaman sa, 

''Ahtoh kinji mai gida ma yayi murnan zuwa na balle su wancan nanka su ɗisi ko basu ji ba su babu damuwa ya'ya na da yayana sunyi farin ciki ahtoh.'' ta fada tana hararan JANNAT da ta cigaba da cin abincin ta kawai.

Dariya duka suka yi sannan nasmah tace anty sadiya abinci'' 

''Wallahi kuwa nasmah barin zo yar albarka na jona ku.'' ta fada tana ajiye jakar ta zuwa dining.

Haka suka ci abinci cikin wasa da barkwanci suka gama sannan aka dawo parlou, kiran sallar la'asar shi ya daga su kowa ya nufi wajen alwala, kamar kullum masallaci su HUDAY suka wuce su JANNAT suka wuce dakin ta ita da sadiya, su nasmah ma suka wuce nasu dakin.

Bayan sun idar da salla ne kuma suka zauna taɗin rayuwa tsakanin su tadin zumunci.

''ina mijin naki Sarkin surutu?'' cewar JANNAT tana kallon sadiya.

"Hmm yana nan yaya! Su ummin sun koma ne?'' 

Sun koma tun satin da ya wuce'', 

ya ya kubran to? ta sake zuwa ta gaya miki wata magana koko?'' JANNAT ta tanbaya fuskar ta na canza wa zuwa ɓacin rai.

''Bata sake zuwa ba tun daga ranan saiday mun hadu da ita a bikin dan gidan yayan su ko kallo ban ishe ta ba ina daga mata gaisuwa bata ma amsa ba!. Sadiya ta faɗa idon ta na cika da kwalla.

''Bazan ce kada ki gaida kubra ba sabida ƙanwar mahaifiyar mijin ki ce ma'ana ita ma uwa ce a wajen shi, yadda bazan zuga ki kiyi wa uwar sa rashin kunya ba haka bazan zuga ki ƙi gaida ƙanwar mahaifiyar sa ba, ki gaishe ta daga haka ya isa idan ta amsa ruwan ta idan bata amsa Bama ruwan ta, haihuwa bake Zaki bawa kanki ba Allah shine zai baki, ban ga dalilin da zai saka mijin ki bai takura miki ba uwar sa bata takura miki ba amma tana ƙanwar mahaifiyar sa ta dame ki dan Allah bai azirta ki ba, ya'ya Allah ke bayar wa,kuma baza mu cire rai ba insha Allah Allah zai baki ki kwantar da hankalin ki ita kuma zaurancen ta kar ya taɓa damunki, da wanne zaki ji shin rashin haihuwar ko kuma surutun ta, na rasa wannan abu har yaushe?mutane basu gane illar yin hakan ne ko me, babu wanda a rayuwar sa baya son ya haifi ɗa kowa yana so yaga ance wannan jinin sa ne, to kuma sai Allah bai baka ba, ba ya fi kowa sanin dalili ba kenan, ga ya'yan ana ta haihuwar su babu wani mutumci a tattare dasu ga yaro har yaro amma ki ga yana shaye shaye,budurwa har budurwa ta zama yar iska , zina yayi yawa maɗigo yayi yawa , liwadi yayi yawa, dan haka karki daga wa kanki hankali, ki gaida ta idan ta amsa ruwan ta idan bata amsa ba ita ta sani , tunda mijin ki bai daga miki hankali ba banga abinda zai saka ki tada hankalin ki ba idan wani ciwon ya same ki mu ke da asara ita bata dashi ahtoh na gaya miki kenan.'' JANNAT ta karisa maganar tana share wa sadiya hawayen da ya zubo mata a kunci.

''Shikenan yaya na gane amma ina tsoron ta ce ya auri salima wallahi bazan dauka ba yaya JANNAT! Zata iya zuga ummi ta fara nuna min hali ko kuma ta saka ummi dole ta sa yaya AHLAN ya auri salima Ni kuma bazan jure ba wallahi!

''Duk abinda kika ga ya samu bawa mukaddari ne daga Ubangiji, tun kafin a halicce ki an rubuta abinda zai faru dake cikin littafin ƙaddarar ki dole ki dauki hakuri , Allah ba azzalumin bawan sa bane Ina ji a jiki na , zaki yi haihuwar da bamu taɓa irin ta ba ma cikin dangin mu dan haka ki kwantar da hankalin ki, ummi na sonki kuma nasan bazata dauki zugan kubra ba''.

''shikenan yaya JANNAT na fahimta Allah ya shige mana gaba! Ameen kanwata'' JANNAT ta fada tana murmushi.

Sadiya ne ta gyara zama sannan tace '' yaya lokacin tafiya kaltanga ya kusa fa ya kamata mu fara shirye shirye gaskiya, tunda a lissafi na an kusa a fara jarabawa a makarantu kinga su nasreen sun kusa hutu kenan.''

''eh haka ne lokaci ya kusa, sai ku fara mana tsare tsaren da suka kamata ,dan gaskiya yanzu ina da abubuwa da ya kamata nayi su, ina daukan su da wasa amma abin ba na wasa bane, babban al'amari mai girma yana tunkaro Ni wanda ko na mutu ko nayi rai haka nake ji a jiki na, amma ina addu'ar ko zan mutu ne akan wannan abin da na saka gaba Allah ya sa sai na kammala shi naci nasara daga karshe ya zare numfashi na'' JANNAT tayi maganar tana kallon sadiya.

Sadiya tayi matukar girgiza dajin wannan lamarin, cikin kiɗima tace '' yaya wanne irin abu ne wannan kenan? Hakan ya na nuna saida rai kenan ko me? Dan Allah kibi a hankali da rayuwar ki, kada kiyi abinda zai salwantar da rayuwar ki baki daya, dan rayuwar ki a jone take da rayuwakan mutane da yawa, ta farko inna na biyu babanmu duk rayuwar su jone take da taki, albarkacin su ƴan kaltanga suka samu, kinga rayuwar mutane da yawa jone take da tasu, haka zalika Ni , rayuwa ta jone take da iyaye na, bayan su banida kowa sai miji tunda ba haihuwa nayi ba, kinga kenan idan wani abu ya same su nima zan shiga mawuyacin hali, rayuka da yawa suna jone ne da rayuwar ki yaya dan Allah ki bar wannan maganar!.

"Bazai yiwu bane sadiya, hakan ba abu bane mai yiwuwa, sabida duka wadannan rayuwakan bazan bari abinda ke faruwa cikin garinnan da kasar nan ya cigaba da faruwa ba, duk da nasan nayi kadan Ni daya na iya dakile wannan Badaqala,amma tabbas zan yi yaki da babbar jjijiya a jikin jijiyoyin bishiyar da ta hana mu zaman lafiya cikin wanna kasar, suka hana mu sha ruwa cikin kwanciyar hankali. Kin ga ta farko ita ce nuwairah, duk yadda kuke tsammanin ta ta wuce nan, hatsabibiya ce ta ainihin gaske, na farko yar maɗigo ce na biyu tana zinace zinace, banda sauran boyayyun sirrukan ta da ban sani ba, domin tabbas nasan akwai wani abu, ga alwashin da take na ganin bayana Ni da ahalina, ina so ko da nuwairah zata yi nasara a kai na da ahalina yazama naga bayan ta daga karshe na kawo duk wani karshen rashin kunyar ta, abu na farko kenan, Shari'a ta da nayi da Hajiya Rasheeda, wata yar kungiyar asiri, bayan gama yanke hukunci ta gudu a gidan yari, aka neme ta aka rasa kafin zartar mata da hukunci, nasan tana nan, kuma ta cigaba da abinda take aykatawa, ina so na binciko su sannan ayi masu hukunci dai-dai ba wai ita kadai ba kawai, harda sauran wadanda suke ayki tare, wannan dalilin ya saka nace maki aiki na na rayu ne ko kuma na mutu, kuma tabbas sai na gabatar dashi domin zaman su cikin al'umma ta hadari ne babba.'' JANNAT ta karisa maganar da dakakkiyar zuciya.

Sadiya dake kallon ta ta dawo kamar mutum mutumi ne ta sauke nannauyar ajiyar zuciya a ranta take faɗin ''yaya ta dabance , kishin al'ummar shine a ranta,ya Allah ka taimaki yaya ta Allah ka bata Sa'a ka kubutar da ita daga hannun waɗannan azzaluman. 

''Ameen JANNAT ta amsa, dan sadiya bata ma san zancen ya fito ba a zuciya take ayyana shi.

Kiran sallar magriba shi ya tada su bayan sun mika farali sannan suka fito falo duk suna zaune har HUDAY din suna kallon tv. suna fitowa HUDAY yace ''Amma kinsan ke muke jira ko? Bamu taba kaiwa warhaka bamu wuce ba kullum da munyi salla muke tafiya, kinje kina ta surutu!

''Wallahi ga wanda ta tsaida Ni kasan sadiya bakin ta ba shiru yake yi ba.'' JANNAT ta fada tana dariya.

To shikenan mu wuce kawia, antyn ma har ta kira way me muke har yanzu bamu taho ba nace mai sunan ta ne ta zo shiyasa.''

Fitowa suka yi duka sadiya ta shiga motar ta ta wuce gida ,su HUDAY kuma suka shiga motar da zai kaisu gidan anty Ishaq ya tada motar sai gidan Hajiya sadiya( kamar HUDAY)

Kullum asabar a can suke cin abincin dare Dukansu dan haka yau ma suka wuce can.

_NUWAIRAH_

Yanda tayiwa Hajiya hari bayani haka akayi, ana isha usama yazo daukan ta, taci kwalliya kamar zata je gasar sarauniyar kyau, cikin riga da wandon ta da suka bi jikin ta suka kwanta, rigar kalar madara wanda kalar jinin kare ja bai shiga ja sosai ba mai duhu, sai gashin kanta da ya sha gyara ta zubo dashi ya rufe gefe da gefen kunnen ta da fuskar ta, ta ɗora hulan kayan irin mai malafa dinnan, tasha eye shadow da eye liner, ga uban eye lashes, Bakin ta ya Sha Jan Baki yana ta kyalli, fuskar nan sharr da ita, mace kawia idan ta kalli nuwairah sai ta sara balle namiji, bata da ƙiba sai uban zubin jiki da Allah ya bata, ga fari kamar zabiya, hannun ta dauke da wayar ta kirar iPhone 11 pro sai dayan hannun karamar jakar ta wanda yayi daidai da kalar rigar, kafata sanye da takalmi flat kasancewar ta doguwa ya saka bata shiru da takalmi mai tsayi,ina kaga nuwairah ta saka takalmi mai tudu, tabbas yan rashin mutumcin suna gaban goshi.

Mahaifin ta da mahaifiyar ta zaune kan kujera a falo, suna kallon tv, kamshin turaren ta shi ya fara kawo wa kofofin hancin su duka sannan ta bayyana.

Tsakiyar su ya shiga ta zauna ta ajiye jakar ta da wayar a kan teburin dake gabansu,hannun ta daya ta saka a kafadar baban daya a kafadar mamar tata, SANNAN tace ''zanyi kewar ku dad amma na sati guda ne kawai, insha Allah idan na dawo zanyi kamar wata 3 a gida haka, bayan na kammala abinda zanyi zamu wuce UK da ku inda za'a saka wa baba kafa, amma yanzu zanje Abuja sati kawai zanyi jirgin 9 zamu bi zuwa Abuja, kamar ko wanne lokaci usama zai cigaba da kula da komai, mom! Ta ƙira sunan maman ta, "na'am yar mom" itama uwar ta amsa.

"Ga kudi nan dubu dari uku ne , ki rike hannunki zuwa na dawo idan basu ishe ki ba Zaki iya yiwa usama magana, akwai komai a gidan ko? Idan babu ki masa magana zai kawo, a bawa dad abinda yake so , da na dawo idan na gama ayyukan gaba na zamu wuce uk dukanmu Abba a saka masa gabar roba Ni a mini DASHEN kunne da ɗan shegiyar nan ya gutsure min(HUDAY)''.

(Hhhh niday mrs Abdull nace duk wanda bai karanta JANNAT na farko ba an barshi a baya🤣)

''To Allah ya bada Sa'a sai kin dawo diyar kirki ki kula da kanki kinji ko?'' mom dinta ta fada tana dafa kafadar ta.

"Karki damu mom, zan yi kokari sosia, "sai na dawo" ta fada tana mikewa ta fice daga parloun.

Motar ta shiga usama ya ja sai airport. 

Suna isa usama ya kira matar deputy ya gaya mata gasu sun iso, dan haka ta gaya masa inda suke , kai tsaye can ya kai nuwairah ya juya.

Zaratan mata ne 6 da kowacce zata yi shekaru 50 amma sabida wayewa da sanin duniya da kuma kudi, bazaka ce ta kai haka ba, sunci kwalliya over ,Dukan su babu wacce take sanye da zanin Dubu goma, kaya ne masu tsada a jikin su kowacce da mayafi da kuma jakar ta a hannu sunsha dauri ya zauna dayday kowacce fuskar ta ta dauki hoda kamar ba tsofi ba, duk kallon su kan nuwairah ya koma dake taunar cingam a hankali tana taku duk jikin ta yana rawa, kamar tana gaban maza haka take taku. Tana zuwa tace ''Sannunku Hajiya''  

Wacce tafi su kyau ita ta amsa da ''yawwa bebe''

Da alama day ita ce shugabar tafiyan.

Guri nuwairah ta samu ta zauna kusa da ita ta cigaba da cin cingam din, karfe takwas da kwata da dare, lokacin. Matar deputy ce tace ''bebe Babu wata Friend naki kamar ki pls yanzu tazo mu wuce?''

Cikin yanga nuwairah kamar tana gaban maza tace '' Hajiya akwai sai dai bansan tana da uzuri ko babu ba, lemme call her.'' 

''ok'' hajiya ta amsa kamar zata rungume nuwairah.

Wayar dake hannun ta ta saka a kunne, kusan second 30 ta fara magana, 

" Leemat ina zee kuna ina ne? Banji me aka faɗa ba a dayan ɓangaren, tace ok'', 

Kiyi mata sallama kawai ki taho zamu wuce Abuja jurgin 9 ne dan Allah ki hanzarta.'' tana fadin haka ta kashe wayar kawai ta jefe a haka


.

Salon ta ya burge su matuka, cikin kasala daya daga cikin matan tace , 

''Hajiya can't wait to go wallahi yarinyar she's so nice.''

Dariya matar deputy tayi sannan tace ''way danma anan ne kika ga hakan idan anje can Abuja a cikin Nicon Hilton otel Zaki tabbatar yarinyar babu wasa. 

Duka dariya suka yi matar tace '' gaskiya I can't wait wallahi.''

Cikin iya kissa da kisisina nuwairah tace '' Kai Hajiya few hours suka rage mata to Abuja sorry.''

Kai nuwairah fa ta na neman haukata wannan mata babu shiri suka ja bakin su dan kada ayi abin kunya a gaban jama'a, dan wallahi kamar ta taso ta fara kissing nuwairah take ji😱

Babu jimawa sai ga leemat,dan haka suka fara cuku cikin nata hanyar tafiyar,basu say bi jirgin 9 ba sai jirgi na Gaba suka bi dan saida aka gama komai ita ma leemat ba dai haduwa ba kam ta hadu over ga kwalliya itama kamar nuwairah. Babu jimawa suka shiga jirgin su ya tashi sai Abuja.✍️




*Mai bukatar JANNAT na farko zai iya

Tuntuba ta don na bashi complete ya karanta domin gane inda aka dosa ta cikin wannan littafin na (tsugunno bata kare ba)*




Kana bukatar lafiya?

(Yawaita azumi)😁



Kafcen ba a haka zai tsaya ba kamar yanda kuka gani a sama zaku ga wani note basai na gaya maku na menene ba wacce ta karanta ta sani, to haka littafin zai cigaba da zuwa muku da abubuwa irin na gyaran jiki da kuma gyara aure da gyara sanwa da kuma gyara muhalli gyaran Addini yanda mutum zai kyautata tsarkin sa da kuma kyautata ibadar sa duk a cikin wannan littafi na JANNAT (tsugunno bata kare ba)


Littafin JANNAT littafin kudi ne game buƙatar karanta wannan littafin daga farko har karshe zata biya kudin ta Naira dari biyu cas ta wannan account din 0009243783 Nafisa Rabiu Umar jaiz bank, sai a turo shaidar biya ma'ana Screenshot KENAN ta wannan lambar 07059305867 ko katin waya na MTN ta wannan lambar 07059305867 hoton katin za'a turo, free PAGES zasu kare ne da nayi page ashirin cif insha Allah. Na fada JANNAT (tsugunno bata kare ba) na kudi ne kar wata ta gaya min maganar wofi idan na gama free PAGES Dan bazan dauka ba a kiyaye. Mai bukatar biya zai iya biya tun daga yanzu domin wanda suka shirya har na fara jin alert, idan na gama free PAGES bazan tsaya ba zan cigaba ne da posting kawai.


#share 

#comment

#Vote

Pls 

Dan girman Allah duk wacce ta karanta tayi share sabida Allah.


*MRS ABDULL CE*✍️


_07059305867_

Post a Comment

ADS HERE
ADS HERE