ADS HERE
Posts

NI DA SHI ABU ƊAYA NE 1to complete


 *بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*


*🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟*




('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.

   ىtɷɾʏ aŋɖ wɾɩttҽŋ bʏ ʑųɭʆa'ų ىa'ҽҽɖ ɩbɾaɧɩm

  ѧҡѧ mamaŋ ųmmҽҽ 😘

ѧҡѧ aųŋtʏ ʑųɭҽҽʏ 💖

ѧҡѧ mataɾ ىaʏʏaɖҽҽ👌



ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )


ҍíՏʍíӀӀɑհíɾ ɾɑհʍɑղíɾɾɑհíʍ.

Godiya ga Allah SWA da ya ba ni ikon fara rubuta wannan littafin. Allah na ke ro'ko yadda ya ba ni ikon farawa, ya ba ni ikon kammalawa lahiya. Ameen.     




*PAGE 1*



  Fuskan ta ca'b-ca'ba da 'kuraje, ga uban 'katotan ciki a gaban ta kamar ka ce kyat ta haihu. 'Kafafuwan ta sun yi wani uban kumbura, wuyar ta kamar mari'kin lema saboda tsabagen rama.


 Le'ban ta sun bushe duk sun farfashe kamar wacce take rayuwa a Sahara.


  Zaune take akan sokawe tana wanke gajerun wanduna da singiletin mai gidan ta. Idan tayi wankin tai wankin, sai ta sake ta cije le'be ta  shafa bayan ta.

   Wani irin bugun 'kofa ake yi kamar za'a 'balle kofar gida Wanda ya saka tai muguwar razanar da sai da abunda ke cikin ta ya dun'kule waje 'daya. Ba kowa zai Mata bugun 'kofar nan ba fa ce Naseer wan da ta mishi la'kabi da Mr Right, Habibi Da'iman, Heaven sent ko kuma 'yallabai. Duk ta na kiran sa da wa'dannan sunan aduk lokacin da ta ga dama.  



"Wallahi na irga uku

 baki zo kin bu'de min kofar nan ba, na lahira sai ya fiki jin da'di tsinanniyar mata kawai".


 Naseer ne ya fa'di hakan da wata irin fusatacciyar murya.

    Kirjin ta ne ya bugu, wani irin tsoro ya lullu'be ta, kasan zanin ta ta kalla sabida wani sanyi da taji, sai ta ga ashe fitsari ta Saki. Da kyar ta iya yun'kurawa  ta mi'ke ta na dafa bango ta isa har kofar gidan ta bude.

   

Gashin kan ta ya dam'ko da 'karfi idanuwan shi sun ka'da sunyi jazur. A matukar fusace ya ce, 


"ke dan kutumar uban ki dama maza kike bi? Wannan abun da ke cikin ki ba ni ne uban sa ba, ko ki fa'di min uban cikin nan ko kuma in kusan kashe ki anan gidan, kuma ba uban da zai tambaye ni dalili".


  Wani irin jiri taji ya na 'diban ta saboda abunda kunnuwan ta ya jiye Mata, wasu zafafan hawayan ba'kin ciki ya wanke fuskan ta da ya yi ba kyan gani saboda 'kuraje, muryan ta na rawa ta ce,


   "Wallahi wanna cikin naka ne, jinin ka ne, ban ta'ba sanin wani 'da namiji a rayuwa ta ba sama dak..."

   Wani irin wal'kiya ne ya gifta a idanun ta, kunnuwan ta suka mata wani duuumm, can kuma ta fara jin kukan tsuntsaye. Dafe kuncin ta ta yi tare da sakin wani marayan kuka ta ce,




   "'Yalla'bai kar Kai min haka, a tunani na duk duniya idan akwai Mai ba da shaida ta to Kai ne, ka sanni, ka San ko ni wacece ka kuma San halina".

    "Karya ki ke yi  karuwa, 'yar iska kawai, wacce ta zubar da 'Kimar ta da aure a kan ta". da 'karfi ya fa'di hakan tare da 'kare dam'ke gashin ta ya ha'da ta da bango.

    Ba ta San sanda ta Saki razanannan 'Kara ba ta rukunkumeshi.

Wani irin jifa ya yi da ita sai da cikin ta ya bugu da tiles din dake shinfi'de a tsakar gidan. 'Dif wuta ya dauke Mata, take kuma numfashin ta ya tsaya caak.

  Naseer bai bi ta kan ta ba ya shige 'daki a matukar fusace, Kai tsaye bedroom ya shige ya jawo durowar mirrow ya dauki biro tare DA yago paper ya rubuta saki, sannan ya zaro belt a jikin wandon jeans din wandon shi ya fito daga bedroom din yai wajan fridge ya dauki pure water da har ya soma 'kan'kara ya fito ya  fasa ruwan nan ya sheka Mata.

   A matukar firgice ta farfa'do tare da wawware idanuwa tana 'ki'k'kifta su. Ba ta gama dawowa daga hayyacin ta ba ta ji saukar belt a jikin ta. Wani 'Kara ta Saki Mai uban 'Kara tare da ru'ko 'kafafuwan shi ta na fa'din.....




Kubiyoni dumin jin yadda wannan cakwakiyar zata kaya.


*Comment and share*




*MAMAN UMMI✍️*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*



🌟NI DA SHI ABU 'DAYA NE🌟


('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.

   ىtɷɾʏ aŋɖ wɾɩttҽŋ bʏ ʑųɭʆa'ų ىa'ҽҽɖ ɩbɾaɧɩm

  ѧҡѧ mamaŋ ųmmҽҽ 😘

ѧҡѧ aųŋtʏ ʑųɭҽҽʏ 💖

ѧҡѧ mataɾ ىaʏʏaɖҽҽ👌



ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )


 

*PAGE 02*



    "Kayi wa girman Allah ka dubi halin da nake ciki ka tausaya min, wallahi ni ba mazinaciya ba ce, duk Wanda ya fa'da maka hakan wallahi so kawai yake yaga ya raba mu, wallahi ban ta'ba bawa wani kai na ba, dan Allah ka dubi maraici na yalla'bai".



    Maganganun da take yi ma kamar 'Kara tunzura shi ta ke yi, janye 'kafafuwan shi ya yi tare da fa'din,


   "Ba'kar munafuka, kalle ki kamar ta Allah amma zuciyar ki fal mugunta ce da she'danci, to bari ki ji wallahi yau ko wa ya tsaya miki sai kin bar gidan nan, matsiyaciya kawai, Allah ya isa tsakani na da ke, kuma kije na sake ki Saki uku tsinanniya kawai".


Ya 'karasa maganar tare da jifan ta da takardan.

   Wani razananniyar 'Kara ta saki, ba ta San ta na da saurin 'karfi a jikin ta ba sai da ta Gan ta a tsaye ta ri'ke shi gam ta na wani irin narkakken kuka.

   Karfin shi ya saka ya ture ta a jikin shi, ba dadin Allah ya ba ta sa'a ta yi saurin ri'ke bango ba da ba 'karamin faduwa za ta yi ba.

   Bu'de kofar gidan ya yi ya hanka'do ta waje ba kin ta sai da ya bugu da siminti, a take kuwa ya fashe ya kumbura yai fushi.

   'Daga kan da zata yi taga ma'kota 'yan gulma dan'kam a kofar gidan ta, alamu ya nuna sun ji duk abunda ke faruwa Dan sun jima a wajan.

   Shiko Naseer bai damu da mutanan da su Kai cirko cirko a wajan ba, ya hau laftar ta da belt 'din hannun shi tare da 'kumduma Mata ashariya ya na kuma aibatata.

   Wata tsohuwa ce ta taho da dauri ta na fa'din,

  


"Nasuru ashe baka da mutunci ban sani ba, yarinya da tsohon ciki ka hau kilan ta har kwar gida jama'a na kallon ka, lallai anyi tujararran 'da a wajan nan. Halan ba uwa ce ta haihe ka ba?".


  Har kusa dashi tazo ta fizge belt 'din hannun shi ta shiga zazzabga masa tare da an taya masa ashariya.

  Har wani jiri-jiri take gani, ga jinin da ya fara bin 'kafafun ta, ta dafe bango ta mi'ke ta saka saurin 'karfin ta ta warce belt 'din da ke hannun wannan tsohuwar ta re da fa'din,

   "Ba'aba Hansai dan Allah ki bar bugun sa, Ina ga wani abun aka masa a waje shi yasa ki ka ganshi a haka, ni Ina kaunar miji na, nasan zuwa anjima zamu shirya kan mu" 

  Galala Ba'aba Hansai ta yi ta na kallon ta, can kuma ta soma tafa hannu ta na sallallami tare da fa'din,


   "Dama abun da ake hi'di akan ki wannan yarinyar (Sunan 'diyar ta ta fari  ta ke da shi, shi yasa ba ta kiran sunan ta ) gaskiya ne? Lallai kin yi asara kuwa, Mai kika Mai 'da namiji? To ga ki nan gashi ai, shi zai yi ajalin ki dama ai iyayan ki ba damuwa su Kai da ke ba, sha sha shar yarinya".

  A cikin 'yan gulma wata ta ce,

   "To  ke ma Ba'aba Hansai ana shiga hurumin Naseer da Mufeeda ne, gashi nan dai kullum cikin wahala ta ke amma ba ta so a fa'di aibin mijin ta".

   'Daya ma tai caraf ta cafke ta ce,

     "Ke ni dama ai sai dai nazo na bawa idanuwa na abinci, na kuma samu na fesawa 'kawaye na a islamiya ".

  Ba'aba Hansai ta ce a fusace,

    "To KO wacce ta wuce gidan ta ko kuma in ciwa yarinya uwayen ta wallahi"

  'Daya bayan 'daya suka fara wucewa, dan kowa yasan masifar Baaba Hansai, amma ba haka suka so ba, sun so suga kwal uwar daka, wasun su ma  komawa su Kai su na le'ke ta Katanga.

   Shi ko Naseer sai huci ya ke yana aiyana irin rashin mutuncin da zai wa wannan tsohuwar Mai masa shisshigi a al'amuran shi.





_Idan kunji daɗi naji commet idan banjiba kowa ya huta🤗_




*Comment and share*





*MAMAN UMMI CE✍️*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*




🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟

('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.


   *STORY AND WRITTEN*

             By

    *Zulfa'u Sa'eed Ibrahim*  (Maman Ummee)



ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ sake) 



*PAGE 03*


 "Ke tsohuwa ki fita a harka ta wallahi, me ye ha'di na da ke ne kike min shishshigi a rayuwa ta? Wannan Mata dai tawa ce ba taki ba, ehe!".

  Kalmar Mata da ya dangan ta Mufeeda da shi sai ya saka ta ji wani sanyi na ratsa zuciyar ta, ke nan ya janye sakin da ya mata, tunda gashi har ya na kiran ta da matar shi.

   Tsohuwa Baaba Hansai kuwa ce wa ta yi,

   "Lallai Nasuru Kai 'din ba ka da albarka, yanzu kalle ni na haihi uban ka ma ba Kai ba, amma har ka iya kallon tsabar idanuna ka fa'di min magana?".



   "To tsohuwa da kin Kama girman ki zan zo har gidan ki in fa'da miki magana ne? Ke ce ba ki ri'ke girman ki ba, Ina ruwan ki da sha'ani na?".



   Girgiza Kai tsohuwa ta yi tare da kallon shi ta ce,

   "Kwarai ka na da gaskiya, amma ka je duniya za ta koya maka hankali, don tunda ba ka ga girman wacce tai sa'a da kakar ka ba, to iyayan ka na gida ma ba neman albarka kake a wajan su ba".


  sai ta mai da kallon ta izuwa wajan Mufeeda ta ce,

   "Ke kuma ki zauna har ya kashe ki wawuyar yarinya kawai, wa ya sani ko asiri ma ya miki".



   "Mufeeda ta ce, 


"ki yi hakuri Ba'aba Hansai ranshi ne a 'bace amma ya na da biyayya, kuma wallahi ba asirin da ya min, ni dai ina kaunar miji na har zuciya da 'bargo na."

   Haushi ya saka Ba'aba Hansai 'kala ba ta 'Kara cewa ba tai hayyar gidan ta. 

   Naseer kuwa belt 'din shi ya 'dauka ya ci gaba da lafkar ta, ta na ihu har cikin ya ke saka 'kafa ya na duka. Sosai jini yake zuba daga 'kasan ta.

  Da taga fa tabbas idan ta tsaya tabbas Naseer zai iya kashe ta, tuni ta soma rarrafe, duk da haka bai bar dukan ta ba har suka fito daga layin. Gashi Safiya ce ko wani magidanci ya tafi nemo na cefane balle ta samu 'dauki daga wani.

   Wani magidanci ne ya fito daga gidan shi, idanun shi suka masa arba da abunde ke faruwa, da Sauri ya 'karaso wajan ya ce,



  "Subhanallah, Malam lafiya? Ba ka da imani ne? Mace da ciki ga jini na zubar Mata amma kake dukan ta da belt".



   "Malam ba ruwan ka, matata ce, kuma wannan cikin ba nawa bane, maza ta ke bi, acikin 'yan iskan da take bi wani ya mata ciki  yau kuma asirin ta ya tonu, ba ka San halin ta ba ne, annamimiya ce, na tsane ta. Uwar ta da ta haife ta ba ta tsugunna ta haifi komai ba fa ce annoba, bala'i da masifa a doran 'kasa, wa ya sani KO uwar tata ma karuwa ce, a can wajan karuwan cin ta ta samo ta aka li'ka wa uban ta".


   Tunda su Kai aure da Naseer ba ta ta'ba jin 'digon kaunar shi ya ragu a zuciyar ta ba, amma yau da ya aiba ta mahaifiyar ta a gaban wani mutumin har ya ke kiran ta da karuwa, sai taji duk fa'din duniya ba bu Wanda ta tsana sama dashi, ba ta ta'ba ganin mahaifiyar ta ba, amma labari yazo Mata akan mahaifiyar ta kamilar ma ce ce, wacce ake alfahari da ita kaf layin su har ake kwatance da ita a wajan sauran 'yan matan layi na wancan zamanin. Yau wani irin wutar 'kiyayyar Naseer ne ke yawo a zuciyar ta, ji take yi gwara SHAI'DAN da shi. 

   'Dago idanu ta yi ta watsa masa wani irin kallon 'kiyayya Wanda sai da ya razana, bakin ta har rawa yake yi wajan furta NA TSANE KA. DA 'dai 'dai 'dai maganganun suka fito.

   Wani yarrr ya ji a cikin jikin shi amma wani irin haushin ta ya yun'kuro masa, ya yunkura zai dake ta, wannan mutumin yai saurin ri'ke shi ya ce,



   "Aboki na ka bi komai a sannu, ka kasance mai bin cike kamin ka aikata Abu, idan ba haka zaka kasance cikin masu DA NA SA NI"

   "DA NA SA NI!!! In dai akan wannan wacce uwar ta tai asarar haihuwar ta ne wallahi bazan ta'ba yi ba".


 Naseer ya fa'din hakan kamar zai yi bindiga.



   "Ni dai shawarar da zan baka idan zaka dauka, ka dauki matar ka kai ta asibi, idan ta haihu sai ai DNA test daga nan likita zai tabbatar maka da abun da ke cikin ta jinin ka ne ko ba naka ba ne, kaga daga nan sai ka dauki Mata ki, amma ba a yanke hukunci Kai tsaye".

   "Kai Malam dakata! Ni ba na bu'katar shawarar ka, domin na tabbata cikin jikin ta ba nawa ba ne, kuma ma ni na riga da na sake ta Saki uku,  ta Kama hanya ta  tafi gidan su Ehe" .


ya na gama fa'din haka ya juya ya wuce.

   Cike da mamakin rashin imanin Naseer wannan bawan Allah ya bi shi da kallo har yasha kwana, ajiyar zuciya ya sauke tare da dawo da duban shi ga baiwar Allah Mufeeda ya ce,



   ''Baiwar Allah sannu, bari na tsayar miki dq adai-dai ta ki tafi gidan ku iyayan ki suga halin da kike ciki, Allah ya saka miki ".

   Mufeeda ba ta iya magana ba saboda azabar da take ciki sai 'daga masa Kai kawai ta yi.

    Napep ya tsayar Mata, da kyar ta iya fa'di masa sunan unguwar su, wajan Shiga ma sai da wannan bawan Allah ya taimake ta. Bawan Allahn nan ya zaro kudi ya bawa Dan adai-dai ta tare da fa'din Allah ya raba lafiya.

   A kofar gidan su ya sauke ta, da kyar ta iya fitowa daga napep 'din jini na bin ta. Girgiza Kai Mai napep din ya yi tare da jan machine din shi yai gaba.

  Tun kafin ta 'karasa kofar gidan ya daka Mata wani uban tsawo ya na fa'din,



    "Wallahi 'kafarki ta taka min dandamalin gida na sai na sabarta ki, shegiya la'ananna. Ooh wato shi mijin na ki ya koro ki sabida abun kunyar da kika jawo, shi ne ni zaki kawo min gida na. To wallahi ahirr 'din ki, ki zo ki wuce duk in da ma zaki ki tafi amma wallahi bazaki zauna min a gida na da cikin shege ba".

   Mufeeda azaba ya ishe ta, domin na'kuda ne ya taho Mata gadan gadan, ga wa'dannan maganganun dake fitowa daga bakin 'kanin mahaifin ta da ya 'Kara jefa ta a tashin hankali. Kallan shi ta yi azaba na nu'kur'kusan ta ta ce,



   "Baba Kai min rai, Ina zani a cikin wannan halin, wallahi Baba babu in da nake dashi sama danan, Dan girman Allah ka da ka kore ni" 

   Kan ta ya taho a fusace ya dinga kwa'da Mata Mari yana fa'din,



    "Wallahi sai dai ki mutu amma ba gida na ba, don Mai zogala ma bazata Bari ki shiga cikin gidan nan ba, wallahi idan ma gidan karuwai zaki koma sai dai ki koma, amma bazaki shigar min gida ba".

    


Tuni mutane sun cika a wajan wasu na zagin kallamu sabida kwata kwata bai ri'ke zumunci ba, bai ri'ke 'yar 'Dan uwan shi a mana ba. Wa'danda ko suka San tantagaryar halin sa, sai dai su yi wa Mufeeda addu'a tare da tausaya Mata a zuciyar su suyi gaba. Dan Kallamu ko 'dan sanda bai Kai shi makirci da sharri ba. Shiyasa kwata kwata ba Mai shiga sabgarshi a unguwan.

   Ba ruwan shi da 'dirkeken cikin dake gaban Mufeeda. Haka ya dauki sanda ya bi ta ya na kwa'da Mata tana tafiya da kyar jini na bin ta, ta na kuma masa magiyar ya rufa Mata asiri ya bar ta ta zauna a gidan sa. Sai da suka fita daga layin har bakin babban titi sannan ya Mata kashe di akan ka da ta Saki ko kyeyar ta ya 'kara gani a gidan sa sannan ya juya.



   Rana ta fito irin Mai shegen zafin nan. Gashi dama rabon ta da abinci tun daran jiya, ga uban jinin da take zubarwa, wani jiri ne ya kwashe ta yuuuu ta fa'di timm bisa cikin ta, dai dai lokacin wata dalleliyar mota Fara Sol ta ja wani dogon birkii ki ka ke kiiiii daf fa ita.







More comment

More typing.




*MAMAN UMMU CE✍️*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*



🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟

('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.

   *Story and written by*

      *Zulfa'u Sa'eed Ibrahim* (Maman Ummee)



ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ ). 



*PAGE 4*



  Da saurin ya fito dan ko iya rufe motar bai yi ba ya na fa'din 

     "subhanallah! Baiwar Allah lafiya???

   Dishi-dishi take ganin shi, can kuma komai ya 'dauke mata difff kunnuwan ta suka do'de, jikin ta ya sake gaba daya.

   A matu'kar ru'de ya cicci'be ta tare da bude motar ya aje ta a back seat, kasancewar fararan shadda ne a jikin sa, sai ya ri'ne da jinin dake zuba a jikin ta, amma shi hankalin shi a tashe, KO lura da hakan ma bai yi ba. Da wani mugun speed ya ke tafiya har ya 'karaso MANAAL SPECIALIST HOSPITAL.

   Cicci'bota ya yi ya na kwala kiran "NURSE! NURSE!! NURSE!!! Where the hell are you???

   Da gudu wata nurse ta 'karaso wasu biyu na bin ta a baya da gadon gungura marasa lafiya. Kwantar da ita suka yi suka gungura ta zuwa wani da'ki, kasancewar shi sananne a wajan shiyasa basu bukaci katin awo ba, amma da badun haka ba ma bazasu kar'be ta ba.

   Kasancewar ya San babu yadda za'ayi su barshi ya shiga, sai bai yi yun'kurin shigan ba, Amman sai Kai wa da komowa ya me yi.

   Doctors har uku ne akan ta, ka na kallon fuskokin su za ka ga tsantsan 'bacin rai a fuskokin su. Daya daga ciki ne ya fito, Kai tsaye ya nufi in da bawan Allah nan ya ke, kamin ma ya 'karasa wajan shi har shi ya iso inda ya ke.

    "Ka biyo no office". Abun da ya ce masa ke nan yai hanyar office 'din shi da sauri.

   A ki'dime ya bi sa, tare ma suka saka 'kafa a office 'din. Zama doctor ya yi sannan ya nuna masa wajan zama shi ma ya zauna.

   Doctor ya kalle shi ranshi a matu'kar 'bace ya ce,

    "Haba architect! Da ilimin ka zaku bari har sai yarinya ta jiga ta haka sannan Ku kawo ta asibiti? Kasan irin jinin da ta zubar kuwa?.

   Gaban shi ya buga daamm bai sai lokacin da bakin shi ya su'buce wajan fa'din,

   "I'm sorry doc ba laifi na ba ne, ita din 'yar gudun hijira ce."

   Doc yai saurin mi'kewa tare da fa'din,

    "Subhanallah! Gaskiya to ta na bukatar taimakon gaggawa domain CS za ai mata, kuma ta na bu'katat jini leda uku, sannan muna bu'katar sa hannun ka a nan."

   Warce takardan ya yi ba tare da wani tunani ba yai signing sannan ya ce,

   "Ba matsala doc a dibi jini na, ai jini na O ne,".

     "To shikenan muje LAB sai a 'diba'.

    A tare suka fit a, cikin 'kan'kanin lokaci aka 'dibi jinin sa. Ita kuwa Mufeeda har an sauya Mata kaya zuwa na tiyata an gungura ta zuwa 'dakin tiyata.

  Da yake kwararrun likitoci ne a kan ta, cikin abinda bai fi awa guda ba aka gama tiyatar.

  Doctor Haroon ne ya fito jikin shi sharkaf da zufa, amma fuskan shi kamar gonar auduga ya 'karaso kusa da architect ya mi'ka masa hannu.

   Shiko Architect da sauri ya kama hannun doc ya ce,

 " doc ya ya ta ke, kun ciro 'dan KO 'yar?"

  Murmushi doc ya yi tare da fa'din,

   "Architect Naseer tunda muke kar'bar haihuwa KO tiyata a asibitin nan, ba'a ta'ba haihuwa irin na baiwar Allah nan ba, wannan matar 'ya'ya biyar muka Ciro a cikin ta, biyu maza uku mata ".

  Wani irin zaro idanu Architect ya yi tare da fa'din  

   "Kai Dan Allah doctor? Inaa take ita? Ta na cikin 'koshin lafiya??"

   Doc ya dafa shi tare da fa'din,

"Ka kwantar da hankalin ka Architect, alhamdulillah ta fita daga hatsari, yanzu haka ma ta na 'dakin hutu an saka mata jini, babies 'din kuma ana gyarasu ne, yanzu ma nazo na fa'da maka ana bu'katar kaya ne."

Architect Naseer ya ce, 

"Alhamdulillah, Bari ka ga nai sauri na sayo kayan".    Bai jira abunda doctor zai ce ba yai hanyar waje da sauri, kwata kwata shi bai ma kalli rigar jikin shi ba, balle ya ga jinin da ya bushe a jiki.

mota ya bu'de ya shiga ya tada tare da yin reverse ya fice daga asibitin. Bai tsaya KO Ina ba sai a wani 'katoton supermarket. Fitowa ya yi yai ciki, bai damu da kallon da mutane ke bin sa da shi ba domin ba ta su ya ke ba. 

    Kai tsaye wajan wataa ma'aikaciya ya nufa tare da Mata magana akan ta taimaka masa wajan za'ban kayan babies quintuplet biyu maza uku Mata. 

  Aikuwa matar nan ta dage ta za'bar masa kaya masu uban kyau da tsada. Wajan biya ATM 'din shi ya mika suka zari kudin su, wasu daga cikin ma'aikatan suka taya shi da kai kaya mota.

   Kaya ne masu uban yawa, domin sun cika both, haka ma back seat hatta front seat ma sai da aka zuba wasu. Juya steering motar ya yi zuwa asibitin. Su kan su nurses 'din ba 'karamin mamakin uban kayan da architect ya siyo su Kai ba, bayan kuma sun San cewa ba shi da wata ala'ka da ita. 

   Tuni har sun gyara yaran sun saka ma matan uku pink din kaya, mazan kuma blue. Ba 'karamin kyau 'ya'yan nan su Kai ba. Labari tuni ya baza cikin asibitin cewa wata 'yar gudun hijira ta haifi 'ya'ya biyar uku mata biyu maza. 

   Architect Naseer kuwa farin ciki ya cika zuciyar sa, ji ya ke kamar shi aka wa wannan haihuwar, ji ya ke Ina ma 'ya'yan sa ne na cikin sa.  Kiran sallar la'asar ne ya ya dawo da shi daga tunanin shi, sai a lokacin ya kalli kayan dake jikin shi, gaba daya ya lalace DA jini har ya bushe.

   Da sauri sauri ya juya ya shiga office din doctor Haroon, minti takwas ya fito yai hanyar motar shi ya fice daga asibitin zuwa masaukin da ya sauka domin yai wanka ya sauya kaya ya rama sallar azahar da la'asar 'din da ya wuce shi.

             6:35PM

  A matu'kar firgice ta farka ta na fizge fizge ta re da fa'din,

   "Na tsaneka Naseer, bazan yafe maka ba, sai ka yi nadama mafi muni a rayuwar ka. Wayyoo Allah na! Wayyooo ciki na, Baba ka da ka Kore ni dan Allah, wallahi babu in da na ke dashi da ya wuce nan".

   Da gudu nurses suka yo wajan gadon suna danne ta, amma still ba ta dai na sambatu ba.  Doctor Haroon ne ya shigo, dai dai da lokacin da Architect yai parking 'din motar sa. Doctor ya shiga duba ta, a hankali kuma sai ta dai na fizge fizgen amma ba ta dai na sambatu ba.

  Architect  Naseer ne ya shigo 'dakin hannun shi ni'ki ni'ki da ka ya, da wani 'katotan flask, dai dai lokacin kuma Mufeeda na fa'din,

   "Wallahi cikin na ka ne 'yalla'bai, jinin ka ne. Naseer ka da ka Kore ni, ka da kamin haka."

   Waro idanu Naseer ya yi, musamman yadda ya ga doctor Haroon na mashi wani irin kallo. Tabbas idan ba kunnuwan shi ba ne suka jiyo masa ba dai dai ba, ji ya yi wannan matar da ya taimaka ta Kira sunan shi. To a ina ta San shi? Shi dai ko mai Kama da ita bai ta'ba gani ba idan ba yau da Allah ga kawo shi ta layin ya gan ta yashe a kan titi ga jini na bin jikin kuma ita ka'dai wajan. Wannan shine dalilin da ya sa ya taimake ta.

   'Karaso wa ya yi ya aje kayan da ke hannun shi, Nurses 'din nan suka gaishe shi, ya amsa musu tare da mi'kawa doctor Haroon hannu. Amsa ya yi but still ya na bin shi da kallon zargi.

   Dan tsaki Architect ya yi tare da kauda Kai, kasa-kasa ya furta, "Wannan shegen kallon zargin da kake min fa ya fara isa ta, idan ka na da magana kawai ka yi".

   Harara doc ya watsa masa tare da mishi kallon zamu ha'du sai ka warware min komai.

  Jan kujera yai ya zauna ya na 'karewa jariran kallo da suka yi matukar kyau a cikin shigan da aka musu na kayan sanyi.

  Doctor Haroon ya kalli Architect ta re da fa'din 

     "ka sa me ni a office". Bai jira yi mai zai ce ba, ya saka Kai ya fice. Nurses 'din ma tuni sun rufa masa baya. Dan tuni Mufeeda ta koma bacci don alluran bai gama sakin ta gaba daya ba. Sam jinin ta bai da 'karfi.





*More comment*

*More typing*



*MAMAN UMMEE CE*✍🏼

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*


🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟

('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.

   *Story & Written by*

      *Zulfa'u Sa'eed Ibrahim* (Maman Ummee)



ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )



*PAGE 5*



  Murmushi architect ya yi tare da mi'kewa ya bi bayan doc. Kwankwasa kofar ya yi sannan ya tura. Zaune ya samu doc ya na duba wasu files, sannan ya na kuma tattara wasu takaddu, alamu ya nuna ya tashi a aiki yana shirin komawa gida.

   Jawo kujera ya yi ya zauna still murmushi kwance a fuskan shi. Gyaran murya ya yi tare fa fa'din 

   'Hey Mr man, ka Kira ni,  kuma gashi nazo. Fa'di cutar ka''

    Harara doctor Haroon ya watsa masa Tara DA fa'din,

   "Wallahi sai kamin baya ni wacece wancan yarinya. Domin alamu ya nuna ka Santa. Allah dai ya sa wa'dancan 'ya'yan ba na ka ba ne'

   "Aikuwa DA nafi kowa farin ciki wallahi, yadda Allah ya saka min 'kauna 'ya'ya ace wa'dancan kyawawan 'ya'yan nawa ne, hmmm Allah ka 'dai ya San irin sadakar DA Zan yi yau 'din nan." Naseer ya fa'di hakan.

   Harara doc ya 'kara watsa masa tare DA fa'din,

   "Look I'm serious Naseer, ka yi min ba ya ni, nasan ka, nasan halin ka, nasan Kai ba mazinaci ba ne, amma mai yasa  take dangantaka da 'ya'yan ta? bayan kuma ka ce min ita 'din yar gudun hijira ce".

   "Aboki na gaskiya akwai abunda na 'boye maka, magana ta gaskiya wannan yarinya ban San ta ba, ban San daga Ina ta fito ba, ni yau ma na me shirin komawa kano wallahi. Na fito daga company DA muke aiki ne ma Zan tafi masauki na, shine na gan ta kwance a akan titi a wannan halin DA nazo da ita. Su nana kuma DA take Kira ta na ala'kantawa DA cikin jikin ta, zai iya zamowa KO mijin ta shi sunan shi Naseer. KO ma dai menene idan ta farfa'do maji."

   Sai a sannan doc Haroon ya Saki wani gwauron numfashi tare DA fa'din,

   "Alhamdulillah. DA na zaci ko abokin nawa ya canza halin da na San shi da shi me."

    Dariya duk suka fashe dashi tare da tafawa.

Mufeeda ba ta gama farfa'dowa daga alluran da aka Mata ba sai 'karfe takwas da minti goma. A hankali take bu'de idanun ta, duk a tsammanin ta zata farka ta Gan ta a cikin kabari, amma sai ta Gan ta a cikin wani daki, ga kuma 'kasan cikin ta dake mata wani azababban zugi.

   Shiko Naseer bai lura ta ma farka ba, ya na nan kusa da quintuplet ya na masu wasa, jin 'ya'yan ya ke yi hat cikin 'bargon shi.

   It's kuwa Mufeeda a hankali komai ya soma dawo mata, wani irin kuka ta kece dashi mail ta'ba zuciya.

A matu'kar firgice ya 'dago ya na kallon ta, da sauri ya 'karasa wajan ta ya na tambayar ta ko lafiya.

KO 'dagowa ba ta yi ba balle ta kalle shi ba. Fita ya yi da sauri ya kira doctor Mansur, domin doc Haroon ya da'de DA tafiya gida. Tare suka shigo shi da doctor. Doctor ya 'karasa wajan ta tare da fa'din,

   "Sannu ko malama. Ya jikin naki? Mai ke damun ki yanzu?"

    A hankali ta 'dago ta kalle shi fuska sharkaf da hawaye ta ce,

    "Nan ke min ciwo" cikin ta ta nuna dai dai inda aka yanka.

   Jinji na Kai doc ya yi, tare da yin rubutu a file din ta, sannan ya kalli architect tare da fa'din,

   "Wannan ba wani damuwa ba ne, a hankali zai Bari in sha Allah."

   Jinjina Kai ta yi. Fita doctor ya yi. Naseer kuwa gadon jariran ya yi ya 'dauko Namijin tare da nuna Mata  fuskan shi cike da annuri. Kamar bazata kalla ba, said kuma ta juyo ta kalli babyn. Gaban ta ne ya bada daaam domin jaririn babu in da ya baro mahaifinshi, hatta wani 'Dan 'digon ba'ki a kumatun Naseer wannan 'da sai da ya 'dauko. A cikin zuciyar ta ta ce, Allah ya raya min Kai a tafarkin sunnan manzo SAW.

   Mai da na hannun shi ya yi ya kwantar tare da 'dauko 'dayan ya 'Kara nuna Mata. Wannan Karon mamaki ne ya bayyana a idanun ta. Gya'da Mata Kai Naseer ya yi alamar kwarai shi ma 'Dan ki ne. Shima sak kamar na farkon harda 'digon bakin kumatun.

   Wannan karan da Naseer ya aje 'dayan matan biyu ya 'dauko ya 'karaso wajan ta. Wani irin waro idanun ta ta yi ta na kallon 'ya'yan kamar a mafarki tare da girgiza kan ta, don't gani take kamar hakan bazai yu ba, Allah da ta tuna da ikon Allah said taji wasu zafafan hawaye na zubowa daga idanun ta.

  Still Naseer ya kuma aje biyun ya 'dauko autar kasancewar duk an musu shaida. Wannan Karon da karfi ta fashe da kuka har da shasshe'kar kuka. Bai San dalilin kukan ta ba, amma haka man yaji zuciyar shi ta karye.

   Mai da 'ya'yan ya yi duka akan gadon su, sannan ya jawo kujera ya zauna kusa da gadon ta, a sanyaye ya kalle ta ya ce,

   "Baiwar Allah, ban sanki ba, ban kuma San daga Ina kike ba, sannan kuma ban San maye matsalar ki ba. Amma na San tabbas ki na cikin wani hali. Idan babu damuwa ki fa'damin matsalar ki ko Zan iya magance mini shi"

   "Waye Kai?" Mai makon ta bashi amsa sai ta jeho masa tambaya.

    "Ni ne wanda ya kawo ki asibitin nan". Ya ba ta amsa.

    "Nagode da taimakon da Kai min, ha'ki'ka da ba dun Allah ya turo ka kai kuma ka taimake no ka kawo ni nan ba, da wani labarin ake yi yanzu. Nagode Allah ya saka maka da alkhairi"

   "Babu komai ai wannan yi wa Kai ne. Ki fa'da min address 'din gidan Ku, sai inje in sanar dasu halin da ake ciki, domin nasan duk in da suke yanzu suna cikin tashin hankali".

    Wannan tambaya da ya Mata sai ya 'Kara tado mata da miki. Ba ta bashi amsa ba sai kukan da take yi .

   Sosai hankalin sa ya tashi. Ya ce,

    "Baiwar Allah lafiya, ko a kwai wata Marsala ne?"

    "Babu wanda ya me neman inda nake, haka kuma kuma babu wanda hankalin shi zai tashi domin rashi na. Ba ni da kowa sai 'ya'ya na". Ta bashi amsa ta na shasshekar kuka.

  Sosai mamaki ya shige shi, ya ce,

   "Baiwar Allah ban fahimce ki ba  Kamar ya ba ki da kowa? Da ma akwai dan Adam 'din da bai da ahali ne?"

   Shuru ta yi ba ta bashi amsa ba amma kuma still ta na kuka. Ya ce, 

    "Dan Allah ki fa'da min damuwar ki, ni kuma na miki al'kawarin in sha Allah sai na taimake ki sai in da karfi na ya 'kare".

    Maganganun shi ya sa taji natsuwa ya shige ta, ta 'dago ta kalle ni sai kuma ta sunkuyar da kai. Kusan second goma sannan ta fara bashi labari tun daga bugun 'kofar Naseer har korar karen sa Baba Kalla ya Mata.

   Sosai ya shiga mamaki tare da jujjuya maganganun ta a kwakwalwar shi, ya ce,

   "Kuma ke kin tabbata 'ya'yan shi be??"

   Ba ta ji mamakin tambayar da ya Mata ba, sai ma murmushin da ta yi a 'Karo na farko sannan ta ce,

   "Sam ni ba mazinaciya ba ce, shi ma idanun sa ne ya rufe shiyasa har ya min wannnan zargi tare da tozarta ni a idanuwar jama'a, amma wallahi 'ya'yan can jinin sa domin hatta waccan 'digon na kan kumatu mazan akwai shi a nashi kumatun, sak mahaifin su suka biyo, kuma ya'kin duniya za'a sake yi a Karo na biyu, bazan bashi 'ya'ya na ba.".

   Ajiyar zuciya ya sauke, sannan ya ce,

    "Dan Allah ina so ki ba ni address 'din gidan Ku."

   Kamar bazata bashi ba, sai kuma ta fa'da masa, saboda irin taimakon da ya Mata bai cancanci ta masa musu ba.

    "Ki kwantar da hankalin ki, zanje gidan Ku yanzu in sha Allah ko mai zai zo da sauki, zaki koma gida ki kula da 'ya'yan ki."

    Sosai ta ji da'di, domin idan har baba Kalla ya'ki amincewa ta dawo, bata San Ina zata nufa ba da 'ya'ya bιyar ba wanda nono ma ba isan su zai yi ba sai an ha'da da madara.




Share & Comment



*MAMAN UMMEE CE*✍🏼

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*



🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟

('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.

   *Story and written by*

      *Zulfa'u Sa'eed Ibrahim* (Maman Ummee)



ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )


  Alhamdulillah! My aminiya is back again with her love and romantic story *KYAUTAR ALLAH* hurry nd buy it. It's just #300 via *0542703718 SA'ADATU ABDULLAHI, GT BANK.* 

    *DON'T WAIT FOR A THIRD PERSON TO GIVE THE STORY, GO FOR THE BOOK YOUR SELF*❤️😍🥰💖



*PAGE 6*



  Bai sha wahalan gane gidan ba saboda Kalla sanannan mutum ne har a gaban anguwan su, can ne sa da gidan yai parking sannan ya fito daga motar tare da mi'kawa yaron da ya rako shi naira dubu. Yaron ya kar'ba ya na murna sannan yai gaba.

Cikin tafiyar shi ta natsattsun muta ne ya isa kofar gidan tare da kwa'da sallama. 

    Kalla na tsakar gida da 'yar 'karamar radio yana sauraron wakar Shata tare da auna tuwan dawa da miyar danyan kubewa a cikin sa. Mai zogala na daga can gyefan shi zaune akan tabarma ita ma ta na auna nata.

    Tsaki Kalla ya ja tare da fa'din,

    " waye kuma wannan zai zo ya damu mutun ya na tsaka da cin abinci? Yanzu haka ma yaronnan ne 'dan gidan Sagiru mai manja, daga jiya na ranci dubu uku a hannun sa, akan idan na samu Zan bashi shi ne zai zo ya tara min jama'a a kwar gida, to ni na fishi tijara wallahi".

   "Kafin ka masa tijara ka jira ka fara jin nawa tijaran. Yanzu Kalla sabida iskanci kasan tun shekaran jiya nake nai man dubu da 'dari takwas nai zubin adashi. Kasan Marwa ta kusa haihuwa, kuma na San kaf unguwar nan jira ake a ga abunda Zan yi, kuma dai ai kasan irin gidan da take aure, gidan manya ne, Ashe har da Kai ake so inji kunya?"

   "Haba mai Zogala ya zaki ce haka?"

    Yo haka ne mana 'Kalla, idan ba haka ba ne to menene?

    Zai bu'de baki ya sake magana aka sake kwa'da sallama. Ya kalli mai Zogala tare da fa'din 

    "ba ri na duba waye, ki ka sani ma KO ku'din ne ya biyo mu har gida".

    Banza tai masa, shikuma ya mi'ke yai hanyar waje ya na su'de hannu har kwar gidan tare da fa'din 

   "waye haka da daddaran nan?"

   Architect Naseer ya ba shi amsa da,

    "Ni ne baba, ina yi ni?"

    "Lafiya in ce dai lafiya yaro?"

    "Eh to baba da dai zamu samu 'dan waje mu zauna zai fi".

   Kamar zai tuttura masa zagi, ko mai kuma yai tunani, sai ya nuna masa dakali tare da fa'din,

   "Muje can mu zauna,  sai muyi maganar, na San dai ba akan maganar nai man aure ba ne, domin ni tuni na aurar da Marwanatu ta na can tana auran 'dan gidan alhj Mika'ilu mai gidan kajin naaan, ai nasan ka sanshi domin shi sanannan mutum ne."

   Haushi ne ya turni'ke zuciyar Architect Naseer, wato 'yar dan uwan shi caan marainiyar Allah ya wula'kan ta, amma ya na koro masa bayanai cewa 'yar shi  ta auri dan gidan mai kaji. Wato yanzu duniya kowa nashi ya sani. Danne fushin sa ya yi ta re da saisai ta muryan shi ya ce,

   "Dama nazo ne akan maganar 'yar ka Mufeeda. Yanzu haka ta na asibiti ta haihu, aiki ma aka aiki. Baba don girman Allah ka yi hakuri Mufeeda ta dado gida ta zauna a wajan ka. Ka ga daganan sai Kai....."

   "Uban waye uban na ka? Ka ga min 'dan iskan yaro. Oooohooo! ashe Kai ne 'dan iskan na ta ke nan da ka mata ciki. To amma dai Kai Allah dai ya 'debe maka albarka har da iyayan ka. Zaka bar min kwar gida KO sai na tara maka jama'a? Dan tijara ne ni da ka ke gani na ana. Tsohon dan tasha ne ni. Wallahi na shiga gida na fito na gan ka nan sai na maka rashin mutunci". Ya na gama fa'din haka fuuu yai ciki gida still ya na sababi.

   Ba 'karamin mamaki ba ne ya Kama architect, guiwa sake ya mi'ke yai wajan motar shi ya shiga tare da reverse ya bar unguwar da sake-sake da yawa a zuciyar shi.

   Mai Zogala ne ta fito ri'ke da tabarya a hannun ta, Kalla na bayan ta da gora. Wayam suka gani. Kalla ya ce,

   "Dan iska da ka tsaya ma na, wallahi da ka koma da rotsattsan Kai.

    Architect bai koma asibiti ba, Kai tsaye gidan aminin shi ya tafi wato doctor Haroon. Kiran shi yai a waya ya ce ya fito ya na waje.

   Fitowa doc ya yi, bai gan shi a harabar gidan ba, gate ya tura ya fito, anan ya ganshi cikin mota. Bu'de motar ya yi ya Shiva tare da fa'din 

   "ya ya dai architect, mai yasa ba ka shigo ba??"

   'Dagowa architect ya yi tare da fa'din,

   "Aboki na akwai fa babbar Marsala?"

  Gaban doc ya fa'di ya ce,

   "Aboki na mai ke faruwa??"

   Architect ya kwashe komai ya fa'da masa. Shi kan shi doc kan shi ya kulle, ya ce,

  "To ya keke ga nin za'ayi kenan yanzu?"

  "Samo 'yar dattijuwa zamu yi wacce zata kula da ita kan nan da sati biyu, ta warware, sai na 'dibe ta ita da 'ya'yan ta mu kuma komawa, wata 'kila KO dan darajar su zai kar'be." Architect ya fa'da.

   "Haka ne. To amma ita ba ta da dangi uwa ne??" Doc ya jeho tambaya.

   "Hmm wannan yarinyar fa abar tausayi ne. Duk yadda akayi a kwai wani babban al'amari a rayuwar ta. Sai dai idan ta bamu labarin ta kaaf. Don shi uban 'ya'yan ma Saki uku ya dan'kara Mata. In sha Allah gobe zanje inyi bincike ta 'bangaran shi, jibi Zan koma Kano, Zan bar maka amanar ta, kwana uku zanyi in dawo."

  "Wannan ba matsala ba ne, yanzu dai bari in koma cikin gida, akwai wata dattijuwa dake wa Sumayya (Matar sa) aiki, sai ita ta kula da ita kawai, domin a daran nan babu in da zamu samu dattijuwan da zata kula da ita". 

    "Hakan ma ya fi, taho da ita kawai sai mu tafi".

   Fita yai ya koma gida, minti goma sai ga doc ya fito shi da Baaba Habiba. Bu'de mata gidan baya ya yi ta shiga, shi kuma ya shiga gaba. Architect ya gai da baaba Habiba, ta amsa cike da fara'a, ya ja mota su Kai asibiti.

   Zaune ta ke ta jingina bayan ta da gado idanun ta a lumshe, tunanuka iri-iri me Mata yawo a kwakwalwar ta, tunani ta ke Ina ma ta dangin mahaifiyar ta zasu 'kauna ce ta. To sun fi baba Kalla ma nuna mata tsana, shiyasa kwata kwata bata kwatanta bin hanyar gidan ba, ita ba ta san menene ma'kasudin wannan tsanar da dangin ta biyu suke mata ba, mahaifinta kuma tun ta na da shekara bakwai ya rasu, ba ta San komai dangane da mahaifiyar ta ba,  Sai dai wani ma'kocin su ne ya ke bata tarihin mahaifiayar ta cewa mutuniyar kirki ce, sam ba ta San mai ya haddasa wannan 'kiyayyar ba.

   'Karar bu'de 'dakin ne ya dawo da ita daga tunanin da take yi, idanun ta ne ya sauka akan nashi, tai saurin sunkuyar da kan ta. Doc Haroon ne ya 'karaso kusa da ita ya ce,

   "My patient mai ke damun ki yanzu??"

   A tausashe ta ba shi amsa da,

   "Wajan 'dinkin ne ya ke min ciwo"

   Doc ya ke. "Okay ba matsala dama zakiji haka, amma in sha Allah zai dai na".

   Architect ya ce,

   "Mufeeda ga Baaba Habiba nan za ta kula da ke daga nan har ki samu sauki a ba Ku sallama, daga nan za asan yadda za'ayi in sha Allah".

   "Nagode Allah ya saka da alkhairi". Ta fa'da hawaye na silalo Mata.

   "To kukan na meye kuma? Idan zaki dinga asarar hawayan ki gaskiya zamu samu Matsala. Kin ji KO?"

   'Daga masa kai ta yi a hankali.

  'Karamar wayar shi ya Ciro a aljihu ya mi'kawa baaba Habiba tare da fa'din,

   "Baaba ni zanje na kwanta, idan akwai wani matsala ga waya nan, number ta ne kawai a ciki sai a Kira ni".

   Baaba Habiba ta ce, 

    "to Allah ya tsare".


            աasɦa ɢaʀɨ 

   Kamar jira ake gari ya waye, mutane wannan ya shiga, wannan ya fita duk 'yan ganin jarirai, har da marasa lafiyar da ke asibitin ma zuwa suke ganin 'ya'ya biyar 'din da Mufeeda ta haifa, ba 'karamin kyaututtuka suke samu ba. Akwai wata da take jinya a asibitin kuma mijin ta babban mutum ne, da aka fada masa, a take ya ce ta ba shi account details 'din ta, sai a Kai sa'a dai dai lokacin architect Naseer sun iso asibitin sai ta ce ba ta da account amma ga yayan ta nan ta nuna architect. Shi kuma ya ba da account number shi, a take yai masu forwarding 'din 2.5m Sosai su Kai masa godiya. Kowa da irin kyautar da ya ke ba da wa. Wasu pampers Wanda a 'Kalla za suyi shekara suna amfani dashi, wasu kuma kayan babies, Kai kyauta dai gashi nan kala-kala.

   Sosai baba Habiba ta ke kula da ita, duk da ance ka da a saka Mata ruwan zafin nan mai uban zafi saboda aiki, amma baba habiba na kula da ita sosai, musamman ta saka aka kawo Mata maganin wanka, sannan kuma wajan tsarki ba ta masa wasa, sai ta tabbatar ta yi shi da kyau.

   Doctor Haroon ya ce zata iya cin komai, sosai ta ke samu abinci lafiyayye taci, ga koko tea 'din da take sha safe da dare. Don yanzu 'yara sun iya Kama nono, sosai kuma suke da ci, gwara ma autar mace, ita ce mai 'dan sauki sauki.

   "Ba ki fa'di sunan da za ai musu hu'du ba da shi ba" 

 Kan ta ta sunkuyar tare da fa'din,

   "Yaya na, na baka wu'ka da na ma, ka saka masu sunan da ya dace" 

  Sosai architect ya ji da'din karramawar da ta mishi, amma sai ya ce,

  "Naji da'di kwarai da wannan karramawar agare ki, amma ke ma nasan dole akwai sunan da kike da mura'di".

   Shuru ta yi, can kuma ta dauki Usainin ta mi'ka masa tare da fa'din,

  "Wannan ka saka mishi sunan ka, shi kuma wancan (Hassan 'din) ka saka masa sunan Mahaifi na (Ahmad) sauran matan kuma autar ka saka mata sunan mahaifiya ta (Zarah) sauran biyun kuma na bar maka za'bi"

   Sosai yaji da'din takwaran da ta mishi. Daukar su ya yi 'daya bayan 'daya ya masu khuduba, sai da ya gama sannan ya dauki babban Wanda ta ce asaka masa takwaran mahaifin ta ya ce,

   "Allah ya raya Ahmad (Abid)" sannan ya kuma 'daga mai bi masa ya ce,

   "Allah ya raya Naseer (Ayaan).

   Gaban ta ne ya ba da sautin duummm, kwata kwata ba ta kaunar 'kara Jin wannan sunan a rayuwar ta, da ta San sunan shi kenan, wallahi da ba tai gangancin ce ma ya saka ma 'dan ta sunan shi ba, amma ya zata yi, ba za ta iya ce masa ya canza ba.

  Shikuwa architect bai ma ga reaction 'din ta ba, idanun shi naga 'ya'yan ta.

   Sai ma nuna babbar ya yi tare da fa'din, 

  Allah ya raya Fatima Zahra (Irfana)

Asma'u (Husna) takwara yai wa mahaifiyar sa,  ita ce ta biyun.

Safiyyah (Shahida) auta kenan.

   "Allah ya raya su a tafarkin sunnah".

 Baaba Habiba ta amsa da 

  "ameen summa ameen"

 Ita kuwa a zuciyar ta ta amsa.

   Tuni architect ya musu sallama akan ya tafi Kano nan da kwana biyu zai dawo. Duk sai take jin ta wani irin. Kwanan biyun da su Kai tare sun Saba don KO da yaushe ya na asibitin.

        вarι мυ waιwaya 'вangaran naѕeer 

   Sai da ta jera masa maruka har guda biyar gyafan hagu da dama, ran ta ya matu'kar 'baci sosai. Ta ce,

    "Da me kake ta'kama dashi? Kyau da dukiya ko? To ka sani, yanzu wallahi idan Allah ya ga dama cikin da'ki'ka sai ya canza maka kamannin ka. Wallahi ba na tunanin akwai yarinyar da zaka samu da za ta Kai wannan yarinya. Sai ka yi nadama Naseer, ranar kuka na man zuwan maka. Kuma wallahi idan wannan ranar tazo ka da ka nuna ka ma sanni balls kazo waje. Ba dai ka yi ma ta Saki uku ba, to wallahi wata daya na ba ka ka fito da matar aure KO in ce ita yar iskar dake hure maka kunne, tunda ita ka dai ka ke gani da gashi a ka. Fitan min a 'daki tun kafin na furta mummunar kalma a gare ka. Wawa wanda bai san ciwon kan shi ba".

   Dafe ya ke da kuncin sa, tabbas mahaifiyar shi ba ta ta'ba 'daga hannu a man shi ba da wayan shi ba said yau. Wutar 'kiyayyar Mufeeda ce ta 'Kara nunkuwa a zuciyar shi. Kuma ya 'kudurta a ranshi babu Wanda ya isa ya saka shi ya kar'bi cikin da ba nashi ba.

   Ficewa ya yi daga gidan gaba daya, dama a waje yai parking motar shi, bu'dewa yai ya shiga tare da firgar ta, bai tsaya a KO Ina ba, sai a wani tamfatsetsan gida. Horn ya yi, mai gadi ya, bu'de masa tare da fa'din 

  "barka da zuwa 'yallabai"

  Wani abu yaji ya tokare masa a wuya saboda sunan da Shafi'u mai gadi ya Kira sa dashi, don't sunan tuna masa yai da Mufeeda, ya na 'daya daga cikin sunan da take kiran sa dashi.

  "Kai shafi'u ka na San ka cigaba da aiki a gidan?"

   "Kwarai kuwa yalla'bai" Shafi'u ya bashi amsa.

    "To matu'kar ka cigaba da Kira na yalla'bai to abincin ka ya 'kare a gidan man". Ya na gama fa'din haka ya ja motar sa yai ciki.

   Nasan masu karatu za suyi mamakindama Naseer ya na da irin tamfatsetsan gida mai uban kyau haka shi ne ya kai matar shi wancan a kurkin. Hmm Ku dai bi ni a hankali, zakuji labarin Mufeeda mai cike da sar'ka'kiya.




*Share and comment*



*MAMAN UMMEE CE*✍🏼

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*



🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟

('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.

   *Story and written by*

      *Zulfa'u Sa'eed Ibrahim* (Maman Ummee)




ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )



*PAGE 7*



   Horn ya yi a kofar 'katotan gate din gidan su. Mai gadi ya wangale masa shikuma ya Danna hancin motar tare da yin parking a wajan aje motoci sannan ya fito hannun shi ri'ke da briefcase ya nufi wajan mai gadin tare da dan russunawa ya gaida shi.

  Cikin fara'a baba mai gadi ya mi'ka masa hannu su kai musabaha tare da fa'din,

   "barka da dawowa Mal  Nasuru, ya wajan aikin?"

   "Alhamdulillah baba mun same Ku lafiya?"

   "Lafiya 'kalau Mal Nasuru, Allah ya maka albarka ya kuma kawo zuri'a na gari."

   "Ameen baba nagode". Naseer ya amsa cike da kunya, don shi mutum ne mai kunya.

  "Baba bari na 'karasa ciki, sai na fito karatu"

  "To mal Nasuru a huta lafiya"

       Cikin gidan ya shige, part 'din hannun daman shi ya fara shiga.

Tun daga shigowar shi har parking 'din motar shi a idanun ta ya yi. Wani irin kyau da kwarjini ta ga ya 'Kara yi Mata. Mai makon ya yo part 'din mahaifiyar sai ya nufi na matar da tafi tsana a rayuwar ta, tuni annurin fuskar ta ya 'dauke, sakin labulen ta yi tai saurin juyawa. Bibbiyu take tsallake steps 'din. Kai tsaye ta fa'da Mata bedroom ba tare da knocking KO sallama ba, a firgice haj Jummai ta juyo a 'Dan firgice saboda yadda aka turo 'kofar ta ce,

   "Lafiya baby? What's wrong with you?".

   Wacce aka Kira da baby ta ba ta amsa da,

   "Mom yaa Nas is back, kuma ya wuce 'dakin wancan munafu'kar matar. Was ya san ko wani asirin zata bashi yau".

  "WHAT!!! ki na nufin Naseer ya dawo? Kuma bai shigo, ya na 'dakin ba'kar munafukar matan can? Noooo bazai yu ba, bazata raba ni da yara na ba, wannan Karan Zan nuna Mata 'karfin uwa". A matu'kar hargitse haj Jummai ta fa'di hakan.

  "Yauwa mom ai gwara kije, idan ba haka ba wannan matar sai ta rabaki da duk abunda kika mallaka, munafuka don taga ita ba ta haihu ba".

  "Assalamu alaikuma" 

   "Ameen wa'alaikumussalam. Muryar wa na ke ji kamar na 'da na Naseer?" Ta amsa sallamar me ya yin da take fitowa daga bedroom. Sanye take da dogon hijjab har 'kasa.

  "Wallahi Umma ta ni ne, dawowa na kenan daga Kaduna na ce na yi missing 'din Umma na da kuma dadda'dan kunun gya'dan ta".

  Haj Zulfah tai murmushi tare da fa'din,

   "Aikuwa kazo a sa'a, don yanzu na gama na juye a flask, daddyn Ku ya ce min zai dawo anjima ka'dan in dama masa, had da alala ma na yi".

  "Kai Alhamdulillah Ummah a kawo min, dama na kwaso yunwa ta". Naseer ya fa'da tare da shafa cikin sa.

  Murmushi ta yi tare da nufan kitchen 'din, ta zubo masa kunun cikin wani cup mai kyau, sannan ta 'bare masa alala a wani 'Dan ma daidai cin plate da yaji kayan ha'di ha'de da kwai a ciki ta ta yayyanka masa da wuka yadda zai masa da'din ci, ta kawo ta aje masa anan tsakiyar center carpet 'din dakin don't ta San shi bai fiye son con abinci a dinning ba.

   Saukowa ya yi ya zauna a 'kasa tare da fa'din,

   "Kai ummah ta ki na ji dani" cup 'din ya 'dauka ya kai baking shi ya kur'bi kunun. Wani gar'din da'di ya ratsa kunnuwan shi ya lumshe ido tare da karka'de kunnuwa irin yadda yara suke yi. Ya kai bakin shi zai kur'bi na biyun kenan aka banko kofar da 'karfi sai da haj Zulfah ta tsora ta. Da sauri haj Jummai ta 'karasa wajan Naseer tare da ka'be cup din kunun da me hannun sa, rabi ya zube a kasa,, rabi a jikin shi. Zafin kunun ya ratsa cinyan shi sai da ya rumtse idanun.

  Ta na huci ta nuna shi da yatsa tare da fa'din,

   "Wato son ni ban isa in fa'da maka magana kaji ba KO? Yanzu ace ka yi tafiya har na tsawon sati biyu, ka dawo amma ka rasa fara shigowa inda na ke sai wajan wannan azzalumar mata mai raba 'da da uwa".

   "Mummyyyy! Haba dan Allah, ita ma fa mama na ce, idan na shigo na gaida ta ai ba matsala ba ne, dan Allah ki dai na kawo wani tunani daban". 

  Hannu ta saka ta make mashi baki tare da fa'din,

  "Dalla yi wa mutane shuru, sha-sha kawai. Dama an riga an gama da kai, an baka abincin da aka yi barba'de barba'de mai zaka game" sai ta mai da kallon ta izuwa ga haj Zulfah da tunda ta fara sababin ta ba ta ce 'kala ba sai ma murmushin da ke kwance a fuskar ta, don idan da sabo to ta saba da rigar uwar gidan ta ta.

  "Annamimiya, dole ki koma gyefe ki na murmushi saboda kin samu abunda ki ke so, kin raba UWA DA 'DAN TA (Sabon littafi na mai zuwa) kuma bari in fa'da miki, idan baki fita al'amura na da na 'ya'ya na ba, sai na miki abunda ba ki ta'ba tunani ba". Ta na gama fa'din haka ta juyo ta kalli Naseer tare da nuna masa hanya. 

   Kallon Umma ya yi fuska a shagwa'be, it's kuma ta gya'da masa Kai alamar ya bi umarnin mahaifiyar shi. Hannu ya saka ya 'dauki plate 'din alalan ya nufi 'kofa.

  Da Saudi haj Jummai ta fizge plate 'din ta yi jifa dashi a tsakar 'daki sannan ta masa dun du a baya ta tura 'kyeyar shi waje.

   Dama Baby na baki 'kofa ta na kuma jiyo duk abunda ake yi a ciki. Ya na fitowa da ita ya fara cin Karo, aikuwa ya sakar mata wani uban harara tare da Jan tsaki yai hanyar part 'din shi domin kayan jikin shi da ya ba'ci da kunu sannan yai wanka ya kuma huta.

  Haj Jummai ta kalli Baby ta re da fa'din,

   " kije ki ha'da masa ruwan wanka".

    Kamar dama jira baby take yi, sai ta bi bayan shi da sauri da tuni shi ya ma shige. Mur'da handle 'din kofar ta yi tare da tura Kai ciki, wani dadda'dan kamshi ya daki hancin ta sai da ta lumshe idanu. Daura 'kafar ta ta yi a kan carpet sai da 'kamarfa ta nutse don taushi. 

   "Yaya Nas akwai tsafta da gayu". Ta furta cikin zuciyar ta

   Wani hoton shi ta 'kurawa ido. Sanye yake cikin suit, kuma a tsaye ya ke, wando ba'ki rigar fari, sai ya ratayo ta sama a kafa'dar shi, dayan hannun shi kuma ya na cikin wando, ya saki tattausan murmushi. Ba'karamin kyau ya Mata ba. Ba'ki ne shi, irin colour 'din black American nan, amma kyakkyawa ne ajin farko. Hancin shi dogo har ba'ka, domin kamannin shi 'daya da daddy har da tsayin, ka na ganin shi like father, like son. Bakin shi 'dan 'Karami dai dai da shi, ga dimple da ya 'Kara masa kyau a duka side chick 'din sa, idanuwan sa ba masu girma ba ne, sannan kuma ba 'kanana ba.

  "Uban me kike min a 'daki? How many times do I have to warn you to stop stepping your legs to my room? Leave now before I chop you into pieces, useless human being" da tsawa ya fa'di hakan da ya saka ta daburce da kyar ta iya gano kofa ta mur'da handle 'din ta fita da gudu sai part 'din mummy.

   Ji ta yi kawai an fa'do mata ajiki. A tsorace ta 'dago tare da fa'din,

  "My goodness, wai me yasa baby ke kullum ba ki da burin da ya wuce ki rin'ka frightening 'dina ne"

  Mai makon ta ba ta amsa, sai ta fashe da kuma. Haj Jummai ta ce,

    "Lord in heaven. Yanzu kuma mai ya faru?".

    Turo baki ta yi irin na shagwa'bar nan ta ce, 

    "To ba yaa Nas ba ne ya min tsawa wai na fitar masa a 'daki".

    Shafa kan ta ta yi tare da fa'din,

   "Its all right, ka da ki damu. KO ya 'ki ko ya so, ke ce dai matar da zai aura".

   With soo much excited ta ce,

    "Mom really??"

    Shafa kan ta ta kuma yi ta re da fa'din,

     "Don't worry my daughter, I'm very sure. Ka da ki damu da duk wani abundan ya ke miki da zaran ya zama naki shikenan." Cike da farin ciki ta rungume haj Jummai tare da ba ta peck a chic 'din ta, sannan tai sama da gudu. Girgiza Kai haj Jummai ta yi ta na murmushi. Sosai ta ke jin 'yar 'kanwar tata a cikin ran ta.


  Wanka ya ke yi, amma gaba daya tunanin Mufeeda ne ke masa yawo, tunanin hanyar da zai taimake ta ya ke. Ya da'de a cikin ba yi kamin ya fito daure da towel a 'kugun shi, days kuma ya na goge man shi. Gaban mirror ya je bayan ya gama goge jikin shi. Man shafawan shi ya dauko mai matu'kar 'kamshi da taushi ya shiga yafawa black shinny skin 'din shi, sannan ya 'dau cumb ya taje gashin shi da ba wani yawa gare shi sai kamshi yake fidda sabida wanke shi da ya yi da mayuka masu matu'kar 'kamshi. Body spray ya fesa kusan Kala biyar, tuni 'dakin ya 'dume da 'kamshi mai da'din gaske. Closet 'din shi ya nufa ya dauko short da vest tare da wata dakakkiyar gezna kalar ruwan goro, sai da ya fara saka na cikin sannan ya saka shaddar. 'Dinkin zamani aka masa ba 'karamin 'Kara fito da kyawun sa 'din kin ya yi ba. Shi kan shi da ya 'Kara kallon kanshi a madubi, sai da ya murmushi. Wajan takalman sa ya nufa ya 'dauko wani half cover 'kalar baki sai shinning ya ke, ga wash stones multicolor masu walwali da akawa saman takalmin kwalliya da shi. Har zai fita haka sai kuma ya dawo ya dauki bakar hula zanna ya murza a kan shi.




*Share and comment*


*MAMAN UMMEEN KU CE*✍🏼

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*


🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟


( _'kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi_)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


_laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadama_.

  *Story and written by*

     *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( _Maman Ummee_)


ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )


 

*PAGE 8*


   Ko da ya fito daga 'dakin shi, sai ya hangi motar daddy a parking space. Part 'din mummy ya nufa. Sallama ya yi sannan ya mur'da handle 'din kofar, ba kowa a palon sai TV da ke ta 'karar banza. Kai tsaye ya hau sama, a 'kofar mom yaja burki tare da knocking. Haj Jummai ta San sai ba baby ba ce, don ita ba 'dabi'ar ta ba ce yin knocking ko sallama, kuma Sam haj Jummai ba ta kwa'bar ta a kan hakan.

   "Yes come in haj" Jummai ta ta fa'di daga ciki a da'kile don ta San wake knocking 'din.

    Tura kofar ya yi ya shiga, zaune ta ke a bakin gado ta na 'da'd'daga lesukan da ta fito dasu daga wardrobe, baby ce ta dame ta akan ta ga wani swiss pitch kuma shi take so ta 'din ka. Zama ya yi gyefan ta tare da daura man shi a kan kafa'dar ta tare da fa'din,

  "Allah sarki mom ba ki missing autares 'din ki ba ne, naga fuskar ki a turni'be".

   "Ba ka na da wacce ta fini a wajan ka ba, so ka tattara a koma can na yafe mata Kai". Ta fa'di hakan ne domin taga reaction din sa. Narkar da fuska ya yi tare da fa'din,

  "Mom pleaseee, a duniyar nan kaf, ni ba ni da kamar ki, ke ce fa kika dauke ni tsawon wata tara a cikin, ki kazo ki ka sha wuya kika haife ni sanadiyar hakan ma kika kamu da hawan jini, sannan kika Raine ni ki ka nuna min so da kauna fiye da sauran 'yan uwa na. To mom a duniya akwai wacce za ta yi kusa da ke ne balle kuma ace har ta fiki. Mom ke ta daban ce a nan". Ya nuna sai tin zuciyar shi.

   Ba 'karamin da'di maganganun sa suka mata ba, sai taji babu wani sauran bacin rai a tare da ita, 'dago man shi ta yi ta masa peck a goshi tare da fa'din,

   "Son Kai da Saudart ban 'kaunar kuna zuwa wajan matar can wallahi, Ku baza Ku ga ne ba ne, poisoning mind 'din Ku ta ke yi"

  Mai makon ya bats amsar maganar ta, sai ya dauko Mata wani zancan daban. Ri'ke cikin sa ya yi tare da fa'din

   "Wasshh Mom i'm hungry, ciki na zafi, juya min yake yi" a shagwa'be ya fa'di hakan.

   Aikuwa da sauri mom ta ru'ko hannun sa ta ce,

   "Muje dinning ga abincin can, dama tuni na saka maid ta ha'da mama favorite 'din ka".

  A tare suka sauko su na 'Dan hirar uwa da 'da har suka iso wajan dinning 'din. Har ya ja kujera ya zauna, mom ta ce,

   "Son please go and get baby, nasan ta na can ta na karance karancan novel" kamar zai yi musu sai kuma ya mi'ke ya nufi 'dakin ta tare da kwan-kwasawa. Daga cikin baby ta ce,

  "Waye ne??

   "Ki fito mom na kiran ki" ya ba ta amsa tare da barin wajan.

   Da sauri tai jifa da takardan sannan ta diro daga kan gadon ta yo waje.

   A dinning ta same su, ita ma ta ja kujera ta zaun.

 "Ya kika zauna kuma? Ki tashi ki serving 'din shi ma na". 

  "No ta barshi kawai, Zan yi da kai na". Yai saurin katse ta tare fa bu'de cooler. Roasted Fish ne ya sa kayan amshi harda irish ga kuma smoothie a gyefe sai tururin sanyi yake yi. Tuni ya ha'diye miyau tare fa fara serving 'din kan shi.

   "Shi kawai za ka ci? Ga fa Paraguay rice nan Baby ta ha'da maka".

Ya ba ta amsa da,

    "No wannan kawai ma ya ishe ni'.

Sosai baby taji haushi duk da ba ita tai girkin ba, don ita ko gas ma ba ta iya kunnawa ba. Kuma ta San saboda mum ta ce masa ita ta yi shiyasa ya'ki ci.

 Babu abunda ka ke ji sai 'karan cokala. Tissue ya 'dauka ya goge bakin shi da shi tare da fa'din   

  "Alhamdulillah". Ya ja kujera baya ya mi'ke.

   "Mum bari naje company na duba abunda ke gudana a can, kin san kwana biyu ba na nan."

   "Hakene gaskiya. To Allah ya kiyaye. Amma na zaci zaka 'dan kwanta ne ka Hutu saboda ka sha hanya" mom ta fa'da.

  "Eh hakene, amma ba da'dewa zanyi ba shiyasa". Sai ya mai da kallon shi wajan baby tare da fa'din,

   "Kije ki gyaramin 'daki na, sauran idan na dawo in ga ba dai dai ba". Da to ta bashi amsa. Shikuma ya fice.

  Kai tsaye part 'din haj Zulfah ya wuce, don tun da bai ga daddy a side 'din mom ba, hakan ya tabbatar mishi a 'dakin Umman shi ya ke. Sallama ya yi tare da knocking. Daga ciki aka bashi izini ya mur'da handle 'din ya shiga.

   Daddy kishingi'de a kan kujera, haj Zulfah na daga gyefan shi, ga dukkan alamu labari take bashi mai sanya nisha'di. Don sai sakin murmushi ya ke yi. Don wannan 'dabi'ar haj Zulfah ne, idan har mai gidan a 'dakin ta ya ke, gaba daya lokacin ta take bashi, haka zata saka shi a gaba ta na masa tausa tare da bashi da'da'dan labaruka masu sanya nisha'di bayan ta gama cika masa ciki da da'da'dan abincin ta. Domim ita gwana ce wajan girki. Duk da ita kan ta haj Jummai 'din ma ba baya ba ce, kawai ita kishi ne ya rude Mata idanu ta kasa kula da mijin ta yadda ya kamata. Kullum sai tashi hankali.

 'Karasowa yayi tare da dur'kusawa har 'kasa ya ce,

  "Daddy Ina wuni? Na same Ku lafiya?"

  "Lafiya 'kalau my boy. Ya ka baro Haruna da iyalan shi??" Daddy ya tambaye shi.

   "Alhamdulillah, sun ce a gaishe ka".

   "Masha Allah Ina amsawa. To ya wajan aikin? Zane ya fita yadda ka ke so?"

   "Eh daddy har ma an fara aikin wajan. Nan da kwana biyu zuwa uku ma Zan koma".

   "To masha Allah. Allah ya taimaka ya kuma maku albarka".

   "Ameen daddy nagode". Sai kuma yai shuru ya sunkuyar da Kai, shi bai tashi ya tafi ba, kuma shi bai ce komai ba.

Murmushi daddy ya yi, don tunda yaga hakan yasan akwai magana a bakin 'dan nashi. Gyaran murya ya yi tare da fa'din,

   "Nasser akwai magana a bakin ka, mai ke faruwa? Ina jin ka. Fa'damin damuwar ka 'da na".

 Haj Zulfah na jin hakan, ta mi'ke za ta bar wajan domin ta bawa 'da da uba waje su ga na. Amma sai ya Mata alama da ido alamar ta koma ta zauna. Ba musu ta dawo ta zauna.

  Gaban shi na fa'duwa, bai San ta yaya daddy zai 'dauki zancan nashi ba. Amma haka ya tattaro kwarin guiwar shi ya soma bawa mahaifin nashi labari tun daga lokacin da ya taimaki Mufeeda har aikin da aka Mata da kuma zuwa gidan su wajan 'kanin mahaifin ta da ya yi. Sannan ya 'karasa maganar da fa'din,

  "Daddy idan har ka aminci Zan 'dauko Mufeeda da 'ya'yan ta zuwan nan gidan, sai ta zauna anan shashan wajam Ummah".

   Mi'kewa zaune daddy ya yi tare da....... 




*SHARE AND COMMENT*


   *_MAMAN UMMEE CE_*✍🏼

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*



🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟

('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.


   *STORY AND WRITTEN BY* *Zulfa'u Sa'eed Ibrahim* ( _Maman Ummee_)



ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )


*PAGE 9*



  "Ban fahimci mai ka ke fa'damin ba son. Ka na nufin yarinya ta haifi 'ya'ya har biyar, sannan kuma iyayan ta sun'ki yarda ta zauna tare da su saboda mijin ta ya sake ta har Saki uku saboda ya na zargin ba 'ya'yan shi ba me?

   "Kwarai haka maganar yake daddy" architect ya ba shi amsa.

    "OK na ji, amma ka ba ni lokaci zanyi bincike a Kai tukun ina da mutane a Kadunar ai. 

  "Nagode daddy Allah ya 'Kara girma". Naseer ya fa'di hakan.

   "Ba komai Naseer, ai 'da na kowa ne, haka ake so ka cigaba da taimako, Kai ma Allah zai taimake ka".

   "Wannan haka ya ke" haj Zulfah ta fa'da.

   Mi'kewa ya yi tare da fa'din 

    "daddy ba ri na duba company'.

    "Ok Allah ya kiyaye, sai ka dawo"

   Da ameen ya amsa tare da yi musu sallama ya fice.


       ѧsıɞıţı 

 Ayaan ne ke ta 'barka kukan nai man abinci, Abid na hannun Baaba Habiba shi ma ya na nashi sai faman jijjigashi ta ke yi. Irfana, Shahad da Husna kuma suna bacci.

   "Baaba Habiba wallahi Allah Ayaan akwai ci ga rashin hakuri, dama dama ma Abid idan na bashi ya sha yana barin rigimar" Mufida ta fa'da.

  "Haka nan zaki ta hakuri, amma dai kam wa'dannan 'ya'ya akwai cin tubarkallah." Baaba Habiba ta ba ta amsa.

  "Aikam suna yin shekara Zan ya ye su ne" ta fa'di hakan ne ta na yamutsa fuska. Ita tasha ganin matan da suka haihu, kirjin su yayi ha'ke ha'ke har suyi ta 'korafi ya na masu ciwo, amma ita Sam ba haka ba ne a wajan ta saboda wa'dannan 'ya'ya masu bala'in tsotso KO bacci bata samun yi, don ma  watarana juya masu baya take yi ta kyalesu da baaba Habiba. 

  Dakyar ta samu suka nutsu su Kai barci ta kwantar dashi ta na ajiyar zuciya. Wayar da Architect ya bai wa baaba Habiba ne yai 'kara. 'Dan kwance zanin ta tai tare da saka hannu cikin lalita ta zaro wayar. Duk da ba ta duba wayar ba tasan mai kiran wayar, don tunda ya ba ta wayar shi ka'dai ke kiran wayar. Ita ma Mufeeda ta san shi ke kiran wayar, wani sanyi taji cikin ranta, don tun da ya tafi sau 'daya ya kira su. Hakan sai ya dame ta. Wanda ya taimake ka ai Kai ma dole ka damu da shi.

   Mi'ko mata wayar Baaba Habiba ta yi, tare da fa'din 

    "gashi Mufeeda 'dauki kamin ya tsinke, kin San ni ba sanin kan wayar nan na yi ba". Kar'bar wayar ta yi kamin ta 'daga kiran ya tsinke. 

    "Laah kin ga kuwa har Kiran ta tsince". Kamin baaba Habiba ta ce wani abu, wani kiran ya 'Kara shigowa. 'Dagawa tai ta Kara a kunnan ta tare da fa'din,

     "Assalamu alaikum."

    "Ameen wa'alaikissalam, ya 'karfin jiki maman quintuplets ?"

 Siririyar dariya ta yi tare da fa'din,

    "Alhamdulillah. Ya gajiyar hanya?"

    "Wai sau nawa za ki tambayi gajiyar hanyar nan ne? Ai nan riga na Saba zirya tsakanin kano da Kaduna, gajiya ai ta bi lafiya. Ina babies 'dina?".

    "Ga sunan sun gama rigima suna barci". Ta ba shi amsa.

    "Ana dai basu abinci suci su 'koshi ko???"

    "Uhmm" kawai ta ce masa.

    "Yaya da uhmm kuma? Ki yi magana ma na. Idan fa ba ki basu abincin su suci su 'koshi zamu samu matsala da ke faaaah, tom".

   Murmushi kawai ta yi. Sosai Mufeeda ta bawa Naseer babban matsayi a rayuwar ta, jin shi take yi kamar wani 'dan uwa, Kai ko a cikin 'yan uwan ma samun irin shi sai an tona, shi mutum ne mai zuciyar zinari, tabbas Mufeeda ta San akwai mutanan arziki a cikin al'ummah, kuma al'kawari ta 'daukar wa kan ta akan bayan iyayan ta to sai wannan bawan Allah a cikin addu'ar ta. Tabbas ya taimaka mata a dai dai lokacin da take ga'bar mutuwa.

 Katse mata tunanin ta ya yi da fa'din,

   "Kin yi shuru. Ina baaba Habiba ta ke?" Amsa ta bashi da,

    "Ga ta can"

    "Ni ma in sha Allah jibi Zan dawo, don doctor Haroon ya fa'damin jibin za'a baku sallama, don't duk kuna cikin 'koshin lafiya." 

Gaban ta ne ya bada sautin daam don tunawa da ta yi zata bar asibiti, kuma tasan cewa baba Kalla bazai ta'ba Bari ta sauna masa a gida ba. Kai ko da ma  ya bari, baaba mai zogale baza,ta Bari ba. To yanzu ina za ta nufa da 'ya'ya har biyar??

  "Hello ko ba kiji abunda ba ce ba ne??" Ya katse Mata tunanin ta.

  " haka ne naji sauki, muna cikin koshin lafiya. Allah kuma ya dawo da kai lafiya".

  "Ameen ameen, sai nazo in sha Allah ko mai zai dai dai ta, ni bawa baaba Habiba wayar"

  Mi'kawa baba Habiba wayar ta yi tare da fa'dawa dogon tunani inda zata samu matsuguni ita da 'ya'yan ta biyar. Hawaye ne suka gangaro Mata, tai saurin sharewa don ka da baaba Habiba da ke waya da architect ta Gan ta tare da jifan tsohon mijin ta da Allah ya isa, don shi ya jefa ta a halin da take ciki yanzu.


   "Muje mana 'yalla'bai, favorite 'din ka ne fa, Avocado juice ne na ha'da maka da pancake, Allah idan ba ka tashi ba zan yi fushi in wuce Abu na ni ka dai inyi lunch 'din"

Sanye take da wando jeans pitch color pencil ne, sai wata arniyar riga kalar ta ba'ka mai shape 'din love ♥ ta gaban rigar, kalar rigar ba'ka, a gaban rigar anyi rubutun cool baby a jiki, sai wasu siraran igiya guda biyi ta bayan wuyar rigar, bayan rigar a fafare ya ke. Fuskan ta simple makeup ne, amma ba 'karamin kyau ta yi ba, kasancewar ta farar mace. 

   Shikuma zaune ya ke akan kujera 2sitter, cinyar shi kuma laptop ne a kai yana tura sako ta email. Aje laptop 'din ya yi a gyefe tare da fa'din,

   "Ooh my princess, wannan wankan na ni kawai ya isa ya rikita ni, na kasa aikin da nake yi" ya fa'di hakan ne tare da janyo ta ta zauna akan cinyar shi, sannan ya zagaye hannun shi ya rungume ta, tare da ha'de goshin su.

 Ashagwa'be ta ce,

   "Pleaseee ka tashi muje dinning. I'm hungry. Your unborn child is also hungry. Do you want him/her to die?"

   "Oh no no no, please stop saying that, you and you child are my world, my joy and My happiness. I can't live without you."

  "Really then let go and eat".

  "OK babe as you wish, cus ur wishes are my command". Ya na gama fa'din haka ya 'daga ta cak, bai aje ta ko ina ba sai dinning. Za ta mi'ke ya mai da ya zaunar ta re da fa'din,

  "Ohh please just sit there, i'm going to serve you today".

 Plate ya 'dauko ya zuba fried superghetti da yaji naman kaza sai tururi ya ke ya zuba. Kallon ta ya yi tare DA fa'din,

  "Zaki sani, ki ka ce kinyi pancake da avocado juice ko"

  Dariya ta yi tare DA fa'din,

  "To Kai ne ai tun tuni nake magiya ka taso muci abinci amma ka'ki sai faman aiki ka ke yi sai ka ce agogo"

   Aje plate 'din ya yi a kusa DA ita sannan ya zagaya ya 'daga ta akan kujeran ya zauna sannan ya zaunar fa ita akan cinyar shi. Fork 'din ya saka ya 'debo taliyar tare DA fa'din,

   "Oya open your mouth".

Bu'de bakin ta yi shikuma ya saka mata taliyar, haka ya dinga 'debowa yai ta ba ta ita kuma ta na ci. Kar'ban fork 'din ta yi a hannun shi ta 'debo taliyar ta Kai baking shi, ya bu'de baki sai ta saka a bakin ta. Cakulkuli ya soma Mata, sai zillewa take yi ta na dariya. Taliyar ta 'Kara debowa, ya kuma bu'de bakin shi, wannan karan ma ta saka a bakin ta, aikuwa ya Kai bakin shi zai tsotse na bakin ta, ta 'kumshe bakin ta GAM.

   "Ina wasa dake? Kin San Allah KO ki bude bakin ko Kuma haahahaa yarinya"

 Hannun ta ke karka'da masa, tana yin baya shikuma yana 'Kara ri'ko ta.

 Naseer! Naseer!! Naseeer!!!

  A furgice ya mi'ke ya na rarraba idanu, caan kuma ya saki mugun tsaki tare DA fa'din,

  "Wannna wani irin iskanci ne haka KB? Kafi kowa sanin yadda na tsani ina bacci a tada ni. Kai banza ne wallahi".

   "KO kuma Kai ne banzan ba. Ka Saki har mutane kazo abun na damun ka, tunda gashi har mafarkin ta kake yi sai sakin murmushi ka ke yi, ai wallahi Nas ka na DA mugun matsala, ba irin shawarar da ban baka ba, amma Kai kunnan uwar shegu da ni. Ai gashi nan tun ba'a jeko'ina ba ka na da na sa ni, wallahi Naseer ka cutar da Mufeeda, kuma wallahi samun irin da wuya a wannan zamanin. Wani iron hakuri ne wannan baiwar Allahn ba ta yi da Kai ba".






*COMMENT AND SHARE*



*MAMAN UMMEE CE*✍🏼

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 


®🏝

 *ZAFAFA WRITTERS FORUM* *...*📚✍🏻

[  ```Zafafa writers is a union for enlightening people to learn hottest things that relate marriage, love and religion.

Zafafa writers is a union to enlight women```]

*https://www.facebook.com/110224494006508/posts/110225604006397/?substory_index=1&sfnsn=mo*


             

  *_Z• W• F•🏝_*




🌟NI DA SHI ABU DAYA NE🌟

('kiʀ'kiʀɑʀʀɑɳ ʆɑɓɑʀi)

  ɓɑɳ yi ɗɑɳ wɑɳʝ kѳ wɑtɑ ɓɑ,  iɗɑɳ yɑ yi รɦigɛ ɗɑ ʆɑɓɑʀiɳ ki/kɑ ɑkɑรi ɑkɑ รɑɱu.


laвarι ne мaι cιĸe da zazzaғan ѕoyayya, yaυdara, cιn aмana тare da 'dυмвιn nadaмa.

  *Story and written by*

      *Zulfa'u Sa'eed Ibrahim* (Maman Ummee)


ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ mʏ 'kawaɭɭɩʏa ɾɷmaŋ ʝa'ɮa (ʍʏ ռaʍɛ saҡɛ )



*PAGE 10*



"Allahu Akbar ya akrami Kabiru. To uban wa ya ce maka mafarkin ta na ke yi? Kuma da ka ke maganar bazan samu kamar ta ba, ai shika uku na yi Mata, ka ga kenan kana iya bin layin zaurawan ta, wata'kila sai Kai DA ce. Wallahi KB ka fita daga idanuwa nan in kulle, ka DA ka sake zuwa min DA maganar wannan shai'daniyar yarinyar a inda na ke. Tunda Ku bakwa ganin abunda ta min sai Wanda ni na Mata. To wallahi idan har ka na 'kaunar tarayyar mu to ka dai na kawo min maganar ta, tom".

  "Hmmm haka dai ka ce koh" KB ya ba shi amsa.

  "Kwarai haka na ce" shi ma ya mayar masa a harzu'ke.

   "To ai shikenan, amma ni ma Ina DA magawa, wallahi duk ranar da Kai na NADAMA ka DA ka sake ka tuna cewa ka na DA wani aboki mai suna Kabiru, domain wallahi babu abunda Zan iya mama. Kuma ma ba wannan ya kawo ni wajan ka ba, Abba ne ke Neman ka, an Kira wayoyin ka duka a kashe. Nagama" ya na gama fa'din haka ya mi'ke ya fice daga dakin.

Tsaki Nasser yaja yare DA shigewa ba yi, shower ya sakarwa kanki, mafarkin DA ya yi ne ya dawo mashi a kwakwalwa. Tabbas duk abunda ya ga ni a cikin mafarkin shi, hakan ya faru lokacin DA suke zaman lafiya DA Mufeeda, soyayyar su ya Fara tariyowa tun daga ranar DA suka Fara ha'duwa. Dogon tsaki yaja tare DA dukan bango. 

   "Sam ni ba ta raina yanzu",ya furta DA 'karfi.



       ⓚⓐⓝⓞ ⓢⓣⓐⓣⓔ 

 Architect Naseer ne dur'kushe a gaban mahaifin shi ya na sauraron abunda ya ke fa'da.

  "Naseer an gama min bincike akan wannan yarinyar DA kake son taimaka wa, gaskiya bata tare DA mutanan kirki, kama ta task cikin 'kuncin rayuwa. Marainiya ce amma ba ta samu iyayan ri'ko na arziki ba. Na amince maka ka taho DA ita idan har ta amince, amma ka Fara 'daukar ta kamar yadda ka ce idan an bash sallama a asibitin, sai ka Kai ta can gidan nasu wajan 'kanin mahaifin na ta, idan har ya'ki kar'bar ta, ka taho DA it's kano kawai."

  Sosai yaji farin cikin amincewar DA mahaifin shi ya yi, duk DA has an damage mahaifin nashi mai taimako ne.

   "Nagode kwarai daddy, Allah ya 'Kara girma da lafiya. Ya kuma sa ka cika DA kyau DA imani". Naseer ya fa'da.

   "Ameen son, yaushe zaka wuce kenan?"

  "Yanzu na ke so na Kama hanya daddy" Nasser ya ba shi amsa

  "To Naseer Allah ya kiyaye hanyar". Da ameen ya amsa tare da mi'kewa ya fice daga 'dakin na nufa 'dakin mom 'din shi tare da sallama ha'de da knocking. Daga ciki mom ta bashi izinin shiga.

  "Ba dai har ka fito ba?" Mom da ke take wa baby kai ta jeho masa tambayaa. Mai makon ya ba ta amsa sai ya ce,

  "Haba mom, wannan yarinyar fa wata rana gidan miji zataje amma har yanzu bata San kan ta na, dubi fa! Babu abunda ta iya sai dai ta kwanta ta karanta novel sai kuma kallon series film. Wallahi akwai gyara a lamarin yarinyar nan".

  "Na ce uban ka kaji ko? Ya zaka shigo min 'daki haka kawai ka hau masifa. Kafa kiyaye ni Nasser. Kuma da lake maganar banza ka ai kai ne mijin na ta na gobe".

  "Ni 'din?" Ya nuns kan shi tare da tambaya.

  "Ah'a ni". Mom ta bashi amsa tare da mama mass harara.

   "Ohh mom please don't even dream about that".

   " Really" mom ta tambaye shi.

   "I can't marry this little spoil brat, and I'm saying the fact."

    "Zan gani ni da kai wa ya haifi wani. Get out of my room. Nonsense!!" Sassautar da murya ya yi tare da fa'din,

    "I'm really sorry mom. I don't mean to upset you, kawai dai ki dai na magana a gaban ta kin San ban San rai ni. By the way, I'm going now. Need ur prayer".

    "Allah ya kiyaye, kuma idan har sai ka na sin my shirya da kai wallahi Naseer sai ka amince da Baby a matsayin matar aure".

    "Mom sai na dawo" peck ya ba ta a forehead tare da wuce wa.

 Ita kuwa Baby tuni dama ta fara hawaye. Ya ba fucewa ta saki kuma mai sauti har da shasshe'ka.

   "Will u stop that nonsense! Ai duk laifin ki ne. Sau nawa nake zaunar fake ina karanta miki abunda yayan ki Naseer ke so, amma nan kike watsar dashii, kuma idan har haka saki cigaba ki na ji ki na ga ni wata zata kwace miki shi, sai dai ki zama 'yar kallo, kuma babu abunda zan iya miki. Ke ya kamata ki wa kanki fighting, ki shisshige masa, ki koyo dabarukan da zaki sake zuciyar shi. Amma kin zauna sai kuka. To ki zauna nan garin kallon ruwa kwado ya miki 'kafa".  Ta na gama fa'din haka ta fice ta bar ta a 'dakin.

  "baby kuwa ha'da kai ta yi da 'gado ta saki kuka tare da jin wani ra'da'di a zuciyar ta.


                *KADUNA*

   Karfe 3:12 ya isa Kaduna, kai tsaye *MANAAL HOSPITAL* ya wuce tare da jin wani nisha'di a zuciyar sa. 

  Parking yai ya fito, kai tsaye office 'din Dr Haroon ya wuce kasancewar tun ya na kan hanya su kai waya ya shaida masa ya na asibiti. 

 Kwankwasa office 'din ya yi tare da turawa 'dauke da sallama a baking shi. Zaune ya ke ya na ta faman rubuce rubuce a laptop ya 'dago tare da ams masa sallamar tare da fa'din,

   "Ahh'a mutumina har ka iso? Gaskiya ka yi sauri" ya fa'di hakn ne tare da mi'ka mass hannu su kai musabahaa.

  "Ni kuma sai nake ganin ma ban yi Saudi ba, don ban yi gudu ba, a normal speed na ke tafiya" Architect Naseer ya fa'di hakan tare da jawo kujera ya zauna.

  "Ka fa'dawa Wanda bai San ka ba, akwai uban da ta kai ka gudu ne a mota". Fa'din Dr Haroon.

  "Ni dai duk mu aje wannan a gyefe, ya patient 'din ta ka da babies 'din ta". Architect ya fa'da.

  "Alhamdulillah wallahi, son 'Dan kwanakin nan ma da haka nan baka ga yadda su da uwar suka murmure ba, wannan dogon wuyar da uwar su ta yi har ya soma cike wa, sai dai fa yaran akwai 'diba, hana ta bacci suke, do ma na sayo mata madara ba bai was baaba Habiba anq ha'da musu dashi, don idan ba haka ba, wallahi ba 'karamin wuya uwar zata sha ba". Dr Naseer y fa'da.

   "Ai 'ya'ya biyar ba wasa ba". Fa'din architect.

  "Yauwa Naseer, ka fara shaida min a waya yadda ku ka yi da daddy. Wai da gaske ya amince ka tafi da wannan baiwar Allah da 'ya'yan ta?" Dr ya tambayi architect cike da mamaki a fuskar shi.

  "Wallahi abokina ya amince, yanzu saura Abu 'daya, gobe ko jibi na ke so mu wuce *KANO*, sai dai wani hanzari ba gudu ba, shin ita zata yadda ta bi ni".

  "To idan ba ta bika ba Ina za ta da 'ya'yq har biyar?" Fa'din dr.

  "Ga shawarar da na kawo, yanzu idan ka rubuta mana sallama, zan kwashe ta ita da 'ya'yan ta a mota, sai muje can wajan 'kanin mahaifin na ta, idan ya hakura to, idan kuma ya na nan a kan bakar shi, sai in lalla'bata muyi *KANO*". Naseer ya fa'din hakan.

  "To shikenan yadda ka CE, hakan za'ayi, yanzu bari na rubuta sallamar sai mu tafi, Dan ni ma zan biku don na zama shaida" dr ya fa'da tare da zaro wata pepar ya soma rubutu.

  "Ni bari na Shiga na duba su". Fa'din architect Naseer tare da mi'kewa ya fita

*_____________________________________*

    "Gaskiya baaba ni dai na gaji da tsotsan Ayaan, duk ya fisu ci wallahi, duk sai 'karar da ni ya ke"

    "Kai *MUFEEDA* kowa ya kalle ki ya San kin ciko kin yi dumurmur dake, 'ya'yan nan basu saki rama ba. Ke ba ki ganin irin cin da kike yi ne yanzu"

 Turo baki rai tare da fa'din,

  "Yoo ai suke kwashe duk abincin da nashi, da naci da sun tsotse, shiyasa ko wani bayan awa biyu na ke jin kamar an min yasar cikin"

  "Gaskiya kam dole kiji kamar ana miki yasar cikin, ai 'ya'ya biyar ba wasa ba" fa'din Naseer da shigowar shi ke nan ya iske ta na korafi.

 Da Sauri ta 'dago ta kalle shi, son ba ta tsammaci zuwan shi a yai ba, wani irin da'di taji da ganin shi. Sunkuyar da kai ta yi tare da fa'din,

  "Sannu da zuwa, ina yi ni ya hanya?"

  'Karasawa yai ya 'dauki Ayaan dake kan cinyar ta tare da fa'din

  "Lafiya qalau alhamdulillah. Ya qarfin jiki?"

  Kai a sunkuye kamar wani sirikin ta ta bashi amsa da lafiya 'kalau.

  "Baaba Habiba ina yi ni, mun same Ku lafiya???"

   "Lafiya 'kalau Nasuru, ya wajan iyayan ba ka, ya ka baro su??"

  "Lafiya 'kalau muka bari su, sunce a gaishe ku. Ya kuma hidima da jikoki??"

  " 'yan jikoki ga sunan tubarkallah sai 'kiba suke abun su".

  Dr Haroon ne ya shigo tare da fa'din,

  "My petient, yau dai dai gida" sai ya mai da kallon shi izuwa ga Baaba Habiba ya CE,

  "Baaba yau dai zaman asibiti ya 'kare, an sallame ku sai gida yau".

   "To to alhamdulillah, ai jikin yai sauki, yara kuma ga sunan Masha Allah". Fa'din baaba Habiba.

   "Gaskiya kam, yanzu baaba sai a fara harha'da kaya, ni ma bari na taya ku da 'daukar wasu cikin mota".

  " To 'dan albarka" fa'din baaba Habiba.

 *MUFEEDA* kuwa tunda akai maganar sallama ta dai na fahimtar ko mai, don gaba 'daya hankalin ta ya tashi, tunani ta fara yi ina zata nufa da 'ya'ya har biyar. Ba tai aune ba ta fara jin saukar zafafan hawaye a fuskan ta. 

   'Dagowar da architect Naseer yai ya sauka akan fuskar ta, har yanzu dai fuskar cike ta ke da 'kuraje. Kallon ta yai na wasu 'yan da'ki'kai sannan yai ajiyar zuciya tare da fa'din,

  "*MUFEESA* ki ba ni dama in taimaki rayuwar ki, na San ki na fama da 'kunci da ba'kin cikin a zuciyar ki, ban San labarin ki kamar yadda na fa'da miki a baya, amma haka kawai na ji ina bu'katar taimakon ki dai dai gwargwadon iya ka ta".

  Sosai ta fashe da kuma mai yin rai. Cikin kuka ta ke fa'din,

   " yaya na kowa ya guje ni, ban da uwa ban da uba, ba ni da bngon jingina, Wanda na dogara dashi, ya wulakantani ya Kore ni, 'kanin mahaifina shi ma y kyamace ni, gwara kowa akan irin tsanan da dangin mahaifiya ta su ke min. Meye laifi na, mai na musu, mai yasa kowa ke kyamatata.*YA ALLAH*" Sai ta kuma rushewa da wani tsumamman kuma da ya firgita 'yan biyar suma a lokaci 'daya suka saki kuka.

   Idanwan shi ne sukaa ka'da su kai jajir, jijiyoyi kan shi duk su kai ru'du ru'du.

  "Idan har cikin zuciyar ki kin 'dauke ni matsayin yaya to ina so ki share hawayan ki, kamar yadda na mi ki al'kawari zan taimaki rayuwar ki da izinin ubangiji. Yanzu ki kimtsa, za muje can gidan 'kanin mahaifin na ki, idan ya saduda ya amshe ki, to idan kuma bai amshe ki ba, ni zan tafi dake"  ya na gama fa'din haka ya fice saboda zuciyar shi da ke wani irin tafarfasa. Wannan zuwan da zai yi wajan 'kanin mahaifin ta ma, don dai ya na son kafa hujja ne, amma da babu abunda za suje su yi a can, daga nan *KANO* kawai zasu wuce.

   Cikin 'kan'kanin lokacin suka gama parking kayan suka kai mota. Baaba Habiba goyi *SHAHIDA* *ABID* kuma a hannun ta. *MUFEEDA* ta dauki *AYAAN* wata nurse kuma ta dauki *IRFANA* ya yin da dr Haroon ya 'dauki *HUSNA*. Dama shi architect tuni ya na cikin mota. Nurse 'din nan ta aje *IRFANA* a cikin mota cikin 'Dan gadon jarirai ta koma cikin, kasancewar dacSEINNA ya zo. Bayan sun shisshiga, doc Haroon na gaba, architect Naseer yaja mota tare da nufan gidan 'kanin baban *MUFEEDA*



*HMMMMM NI KUWA MAMAN UMMEE NA CE ASHE ZA'A KWASHI 'YAN KALLO KENAN A GIDAN KALLAH*


  *COMMENT DIN KU SHI ZAI BA NI DAMAN SUBURBU'DO MUKU NEXT PAGE, JIN SHURU YA NA NUFIN AJE TYPING*



*MAMAN UMMEEN KU CE*✍🏼

Post a Comment

ADS HERE
ADS HERE