ADS HERE
Posts

DOGARI PAGE 4

DOGARI na Maryam Muhammad Hasheem (M jaruma) Aliyu bangaransa ya wuce ya zauna falonsa yana tunani, tambayar kansa yake yi "Anya nayi wa Rayhan adalci kuwa, ina tsoron karta mutu a dalilina" Wayarsa ce ta yi ringing, ya dauka ya duba allon wayar, Shukhrah ce ta kira shi, wani farin ciki ya ziyarci zuciyarsa, wayar na gama ringing ya kirata, suka shiga hirar soyayyar su Kiran General ne ya shugo wayarsa ya yi sauri ya amsa "Hello sir" "Ka zo ka same ni a falo na" "Ok Sir" Aliyu ya katse wayar ya mike ya fita General zaune a falonsa Aliyu ya shugo cikin sallama, sai ya kame alamar girmamawa, General nuna masa wurin zama ya yi "Zauna" Aliyu ya zauna babu musu Genaral ya ce Aliyu ka yi hakuri da abin da zan fada maka, Rayhan ta ce ba za ta iya auranka ba, yanzu zan mayar maka da sadakinka, saika kira iyayenka ka fada musu an fasa auran General ya mika masa wani takarda "amsa" Aliyu ya tashi ya je ya amsa "Wannan takardan transfer ne, na yi maka transfer zaka koma katsina da aiki" Wani farin ciki Aliyu ya ji ya ziyarci zuciyarsa sai kuma ransa ya bace saboda Nisan da zaiyi da Shukhrahn shi, sai kuma ya ce kwana nawa ya rage mu kasance tare Bayan General ya gama duk bayanan da zaiyi sai ya sallami Aliyu ya tafi Rayhan yana komawa bangaransa Shukhrah ya fara kira ya fada mata anyi masa transfer, ta nuna damuwarta a zahira but a zuciyarta farin ciki ta yi zata sakata ta wala abinta Saiya kira iyayensa ya fada musu babu aurenshi da Rayhan, mahaifiyarsa ta ji haushi sosai don tana bala'in son Rayhan, sai kuma ya fada musu anyi mishi transfer zuwa gida katsina, gobe yana nan zuwa Rayhan tashi ta yi ta je ta saka kin dakinta sannan ta dawo ta zauna kan kujera ta fara kuka mai matukar taba zuciya, tana tuna soyayyar da Aliyu yake nuna mata da kalamar bakinshi "Aliyu ashe duk yaudarata kake yi, Aliyu ashe baka sona, me na yi maka, kasan yadda nake sonka kuwa" Rayhan ta yi kuka me isanta har ta ji ba dadi Da daddare Aliyu ya je wurin Shukhrah suka sha hirarsu, suka yi bankwana, Shukhrah harda kukanta jinajina wai kada ya tafi ya barta, haka ya yi ta rarrashinta, ya samu hankalinta ya kwanta sannan ya baro wurinta Washegari Aliyu ya gama shiryawan shi tsab ya shugo harabar gida yana son ganin Rayhan amma babu dama, ya dade a tsaye yana kallan gidan, yana tuna abubuwan da suka faru, fito da wayarsa ya yi ya shiga rubuta mata text message, bayan ya gama ya tura mata sannan ya zuba kayayyakinsa a motarsa ya yi wucewarsa Rayhan kwance kan gado cikin matukar damuwa da kadaici, sako ya shugo wayarta, ta dauki wayar ta bude sakon, ta shiga karantawa *Assalam Rayhan! dafatan kin tashi lafiya, na rubuto miki wannan sakon godiya daga kasar zuciyata, na gode da halachcin da kika min a rayuwa, ba zan taba mantawa dake ba a rayuwata, zan tafi Rayhan, ina miki fatan alkairi* Rayhan ta fashe da kuka fadi take "Don Allah karka tafi ka barni, wallahi ina sonka" Tashi ta yi da sauri ta fita, ta shugo falo da sauri, ta kara yin hanyar waje, ta shugo harabar gida dai dai motar Aliyu na fita daga gidan, bin motan ta yi da gudu tana kiran Sunanshi "Aliyu karka tafi ka barni, ka jira ni mu tafi tare" Aliyu bai jita ba, ya yi mata nisa sosai, ta zube gwiwowinta a kasa tana kuka kamar zata mutu, ta yi kukanta me isanta daga karshe ta bawa zuciyarta hakuri ta koma gida A ranar kanwar mahaifiyar Rayhan wato Haj Karima tazo, hankalinta ya tashi sanadiyar halin data samu Rayhan, Aliyu gida kankiya ya wuce, yana isa ya fara zuwa fada ya gai da mai martaba sarkin kankiya, sannan ya dawo bangaren sa ya tarar da mahaifiyarsa Haj Amina da Habib da Amira, sun yi farin cikin ganin shi Haj Amina ta ce ina Rayhan? Shuru Aliyu ya yi sai data kara tambayar sa a karo na biyu sannan ya dago ya kalle ta "Tana gidansu" "Allah sarki, Aliyu na so ka da Rayhan, Yarinyar kirki, zanyi farin ciki idan ta kasance sirikata" Amira ta marairaice "Don Allah yaya ka auri Aunty Rayhan ni ina sonta Yar murmushi ya yi ya ce to ai ita ce bata sona, ita ce ta janye maganar auranmu, ta ce ni ba ajinta bane Haj Amina ta ce kai Aliyu bana tunanin Rayhan zata yi haka Habib ya ce nima wallahi Yaya Aunty Rayhan tana birge ni Maganarsu ji ya yi yana kokarin sa mishi ciwon kai sai ya ce wai ina Umar ne? Amira ta ce yana katsina ya je bikin abokinshi Mikewa ya yi "Bari na je na watsa ruwa a Jikina" Ya fice ya barsu Bangaren shi ya wuce, yana isa ya shiga bayi yai wanka sannan ya fito yasa kananun kaya marasa nauyi, sai ya shigo falonsa ya zauna ya dauki waya ya shiga neman numbern Shukhrah amma yana shiga bata dauka, yi ya yi kamar zai zare, hankalinshi ya tashi, ya tashi ya shiga yin safa da marwa yana kara gwada kiranta, ya kirata yafi sau Ashirin amma bata dauka ba Ta bangaren Shukhrah kuwa tana tare da Alh Badamasi a Hotel suna sheke ayansu, duk lokacin da take tare da abokin harka a silent take saka wayarta, bayan Alh Badamasi ya sauka a kanta, daukar wayar ta ta yi taga missed call din Aliyu, hankalinta tashi ya yi, mikewa ta yi tana kokarin mayar da kayanta ta Alh Badamasi ya kalleta "Miye kuma kike wani mayar da kaya?" "Tafiya zanyi" Bata rai ya yi ya ce bangane zaki tafi ba, sau biyu fa na yi, saura daya Galla masa harara ta yi nidai zan tafi kawai ka sallame ni "Haba kar muyi haka dake mana" "Ni gaskiya ka sallame ni" Daukar wandonsa ya yi yasa hannu a aljuhun wandon ya ciro dubu biyar ya mika mata Ta rike kugunta "ba dubu goma muka yi da kai ba" Ya ce kuma ai sau uku muka yi dake zanyi Jan tsaki ta yi ta fisge dubu biyar din tana fadin Allah ya isa tsohon banza Alh Badamasi ya yi yar dariya "ai Allah ya isan karuwa bai karbuwa" Shukhrah ta fita cikin fushi, tana fita harabar hotel ta kira Aliyu, bugu daya ya dauka ya fara masifa "Ina kika je kika aje waya duk nabi na damu, kinsan halin dana fada kuwa" "Ka yi hakuri mijina, bamu da wuta ne, shine nakai caji, zuciyata ce ta bani ka kirani sai yasa ma nazo na amsa wayar" "Zan tura miki kudi ki sayi power bank ki dinga cajin waya, bana son na kara kiranki baki dauka ba ko na ji wayar a kashe, kuma bana son yawo, a samu almajiri da zai rika zuwa aike, zan dinga biyanshi, nifa masifar kishi nake dashi, Baby kar kiji haushina" Wani ajiyar zuciya Shukhrah ta yi "to nidai ka yi hakuri kuma zan kiyaye insha Allah" "To dakyau matata" Suka cigaba da hirarsu cikin soyayya Haj Karima tana matukar debewa Rayhan kewa, Rayhan jinta take kamar mahaifiyarta Rayhan kwance kan gadonta hawaye na fitowa daga idanunta, rike take da wayarta tana kallan numban Aliyu, zuciyarta na raya mata ta kirashi, sai ta yi kamar zata danna Kira amma sai ta dakata, daga karshe jefar da wayar ta yi ta fashe da kuka, kirjinta na zafi hakama kanta, Haj Karima ta shigo, da sauri ta hau kan gado ta rike Rayhan "Rayhan meke faruw...." Haj Karima ta dakata sanadiyar jinin dake fitowa ta hanci Rayhan "Inna lillahi wa Inna ilaihir raji un Rayhan Rayhan" Rayhan ta ce Aunty zan mutu "Rayhan ba zaki mutu ba" Rayhan ta rungume Haj Karima tana kuka Haj Karima ta tashi ta shiga bayi ta dakko tissue sannan ta dawo ta shiga gogewa Rayhan hawaye da jini, bayan ta gama taje ta yar da tissue din sannan ta dawo ta shiga rarrashin Rayhan harta samu ta yi shuru "Yanzu ki fada min meke damunki?" Rayhan ta girgiza kai alamun a'a "Aunty bakomai" "Ya zaki ce min babu komai, taya zan yarda" "Aunty don Allah ki daina tambayata, yana kara min damuwa, ki barni kawai" "To shikenan zan fadawa mahaifinki ya tuntubeki akwai abinda kike boyewa" Rayhan ta rike Haj Karima da sauri "karki fada mishi don Allah, ki taimake ni ki barni kawai" Haj Karima ta yi shuru tana kallan Rayhan cikin tsananin tausayi Haj Karima ta kira family doctor yazo ya duba Rayhan, ya tabbatar da ta kamu da ciwon zuciya, hankalin Haj Karima ya tashi sosai, Likita dai ya bayar da magungunar da zata rika amfani dashi Washegari Aliyu ya tafi Katsina inda ya dawo da aiki, haka rayuwa ya cigaba har tsawan wata daya, Aliyu ya manta da Rayhan, auransa da Shukhrah ya gabato Rayhan ta dan fara rage tunani, kuma damuwar da take ciki bai hanata cin abinci, cin abincin ta har mamaki yake bawa Haj Karima, ga tsinannan kwadayi, ita ce chocolate ita ce sweet yau General zai yi tafiya zuwa America, Rayhan da Haj Karima sun rakashi iya harabar gida inda motoci da sodoji ke tsaya suna jiranshi, General ya Kalli Rayhan "Sweetie na ki kula min da Kanki" Rayhan ta lumshe ido "karka damu Dad, ni dai fatana Allah ya dawo min da kai lafiya" "Amin yata, kuma banda tunani" Ya kalli Haj Karima "ga amanar Rayhan ki kula min da ita don Allah" "Karka damu, Rayhan yata ce" Murmushi ya yi "to sai na dawo" suka ga tafiyarsa Sannan suka dawo suka zauna a falo, Haj Karima ta kurawa Rayhan ido "Kamar kin kara jiki" Rayhan ta ce ba kama bane nima nasan na kara kiba, akwai wani atamfa na riga da siket yana shiga na fa amma jiya da nazo sawa yaki shigana Haj Karima ta ce lallai hankalinki ya kwanta, kin daina tunani Rayhan ta ce "uhmm Allah kadai yasan karatun Bebe" Bikin Aliyu da Shukhrah ya rage saura sati daya, Shukhrah fa babu kwanciyar hankali, tana shiga tana fita wajen neman magungunan matsi, da kayan mata, ta gyara fatar jikinta ya yi fari, ya yi kyau da taushi, ta canza sosai A katsina Aliyu ya siya wani dan madaidaicin gida, two bedroom plat, ya yi gyare gyare a gidan, gidan ya yi matukar kyau sosai Can gida kankiya kuwa sai gyare gyare ake ta yi a masarauta, kowa na farin ciki amma a zuciyar Haj Amina da Amira sun so ace Aliyu Rayhan zai aura amma kaddara ya riga fata, sai suka fauwalawa Allah komai Rayhan kwance kan gado, rike take da wayarta, fito da numban Aliyu ta yi, ta tsaya tana kallan sunan da ta yi saving dashi "heartbeat" wasu hawaye masu zafi suka shiga fitowa daga idanunta, goge numban ta yi daga wayarta gabadaya, a hankali ta furta Aliyu na hakura da kai har abada, tunda muka kai wannan lokacin baka dawo ba, nasan ba za ka taba dawowa ba Share hawayenta ta yi jin alamun za'a shigo, Haj Karima ce ta shigo a rikice cikin kuka tana fadin "inna lillahi wa inna ilaihir raji un" A firgice Rayhan ta sauka daga kan gado "Aunty meya faru" Haj Karima ta cigaba da kuka tana salati "Na shiga uku Aunty ki fada min meya faru?" "Mahaifinki Rayhan" Rayhan ta zaro ido cikin tsoro bakinta na rawa "meya faru da mahaifina?" "Jirginsu ya yi hatsar....." Wani ihu Rayhan ta yi sannan ta yanke jiki ta fadi, Haj Karima tayi kanta "Inna lillahi wa inna ilaihir raji un" "Rayhan Rayhan, ki tashi Rayhan" ko motsi Rayhan bata yi, Haj Karima ta mike da sauri ta dauki wayarta ta kira Family Doctor bada dadewa ba sai gashi yazo ya sami Rayhan jini na fita ta hancinta, treatment din Rayhan ba zai yu a gida ba, motar Asibity ya kira, bada dadewa ba sai ga motar ya zo, aka tafi ta Rayhan Asibity Allah dai ya yi wa General Muhammad wali rasuwa wato Chief of army staff rasuwa sanadiyar hatsarin jirgin sama, anyi jana'izan sa, an amshi sarakan uku Rayhan na asibity bata farfado ba Aliyu tun washegarin ranar da General ya rasu ya zo Abuja ya yi gaisuwa, bai damu da ya ga Rayhan ba ko ya damu da halin da take ciki, damuwarsa Shukhrah, wurinta yaje suka sha hira, ya ga yadda ta kara kyau, ji yake kamar ya cinye ta tsantsar soyayyar da yake mata Aliyu ya yanke shawara tunda auransa da Shukhrah ya rage saura kwana uku ba sai ya koma Katsina ba, zai jira bayan an daura aure sai ya taho da amaryarsa Babban abokin Aliyu wato Abdulrahman likita ne, a London yake aiki, yana zaune da iyalinsa a can, ya shigo Nigeria domin bikin abokin nasa Aliyu Aliyu ya yi farin ciki da ganin Abdul sun taba hira sosai, ranar dai Aliyu baki har kunne Tun ana gobe daurin aure yen uwa maza da abokan Aliyu da masu amsar aure suka taho daga kankiya, Aliyu ya kamawa kowannansu dakin Hotel Shukhrah kuwa ta tara yen uwa yen bariki a matsayin yan uwanta, bafulatanar Adamawa ce, iyayenta da danginta na can Adamawa, tunda ta tashi bata jin magana ita ce zuwa gidan solo wato gidan gala, ta je wurin wannan saurayin ya yi wasannin banza da ita ya bata dari biyu, taje wurin wancan in ta yi sa'a ya bata dari biyar, Sahabi dan unguwansu ne, tun daya gano bata jin magana yar hannu ce sai ya fara janta da soyayya har ya fara kaita dakinsa yana kwana da ita, tana jin dadin Sahabi sosai saboda irin soyayyar da yake gwada mata, bai taba bata ko naira daya ba, sai Idan ta je ta yi iskanci da wasu sai ta kawo masa, da zai koma Abuja inda yake lebiranci ya hurewa Shukhrah kunne akan Abuja akwai kudi sosai, ta bishi su gudu taje ta sami kudi, haka kuwa ya faru, ta bishi zuwa Abuja, gidan Gala ya kaita tana rawa tana samun kudi suna rabawa tare, ta yarda Abuja akwai kudi don a Adamawa Idan namiji ya kwanta da ita dari biyar yake bata Idan ya yi tsada dubu daya duba daya da dari biyar, Idan ta hadu da me kirki ya bata dubu biyu amma anan Abuja Idan namiji ya kwanta da ita tana samun yar dubu biyar zuwa goma, watarana tana kwanciya da maza suna kaiwa takwas a rana watarana goma sai ta tashi da kudinta masu nauyi, zuwa anjima Sahabi yazo ya amshe, haka suke rayuwa An daura auren Aliyu da Shukhrah a kofar gidan magajiya, bayan daura aure ne aka fara shirye shiryen wucewa Katsina Sahabi tunani yake ta yi kenan Idan Shukhrah ta wuce wa zata rika ciyar dashi, hakan yasa ya yanke shawarar binta katsina, hakadai aka dauki Amarya zuwa katsina Anyi addu'ar bakwai na Genaral an gama, kowa ya water, gida ya rage babu kowa, Haj Karima da Rayhan suna Asibity Rayhan kwance kan gadon jinya har yau bata farfado ba, Haj Karima zaune gefenta tana kallanta tana hawaye A hankali Rayhan ta bude idanunta, ganin ta farka yasa Haj Karima ta mike da sauri ta je ta kira Likita, da zuwan likita ya shiga yiwa Rayhan gwaje gwaje ya tabbatar da lafiya lau Haj Karima ta yi wani ajiyar zuciya "sannu Rayhan" Muryar Rayhan na rawa "Aunty ina Daddy na?" Haj Karima ta rufe fuska tana kuka, Rayhan ta fashe da kuka don hakan ya tabbatar mata Dad dinta ya rasu fadi take Allah ya jikanka Daddy, Allah ya gafarta maka, Mummy kin tafi Daddy kaima ka tafi, kun barni ni kadai, ta cigaba da kuka kamar ranta zai fita, Haj Karima tana kuka tana rarrashinta Bayan kwana biyu Rayhan ta dan murmure, suka dawo gida su cigaba da jinya Rayhan zaune a falo ta jingina da a kujerar da take zaune, mai hidimar gidan ta shigo da farantin kayan marmari ta aje a gaban Rayhan, tsabar tunanin Rayhan bata sani ba, Haj Karima ta shigo ta same ta "Rayhan" A firgice ta kalli Haj Karima "Na'am Aunty" "Tunani kike yi ko?" "A'a kawai ina tuna Dad ne" Ta zauna gefenta "addu'ar zaki yi masa, shi yake bukata" "Allah ya jikansa" "Amin" "Amma Rayhan na tambayeki mana" "Ina jinki Aunty" "Kin san kina dauke da juna biyu" A rikice Rayhan ta zaro idanu cikin tsoro ta juyo tana kallan Haj Karima, itama kallanta take yi *DOGARI* Rayhan na kallan Haj Karima bakinta na rawa ta ce Aunty ciki fa kike nufi "Eh shi" "Taya na samu ciki?" Haj Karima ta ce kinfi kowa sani, ba'a taba samun ciki haka kuma ba'a sha a ruwa dole sai da dalili Sai Rayhan ta fashe da kuka "Aunty na shiga uku, ya zanyi da rayuwata" "Asibitin da kika kwanta basa cire ciki da tuntuni ma an cire amma yanzu dai kawai zamu sami Asibitin da suke yin abortion ne sai muje su cire" Rayhan ta kalleta da sauri "Aunty ba zan cire ba zan haifi abina" "Haba Rayhan me zai kai ki haihuwar dan da bashi da uba, bana goyon bayan haka, kuma abin kunya ne a zuri'ar mu" Rayhan ta ce Aunty dana yana da uba "Waye ubanshi?" Shuru Rayhan ta yi tana tuno Aliyu, sai hawaye ya taru a idanunta, Aunty ta dan dafa kafadanta "Yi hakuri Rayhan, ki daure ki fada min waye mahainsa?" Rayhan ta dago ta kalleta "Aliyu" "Waye Aliyu?" "Wanda zan aura sai aka fasa auran" "To yanzu saiki kirasa ki fada masa" Da sauri Rayhan ta ce a'a Aunty ba zan taba bari ya sani ba, matarshi tana da kishi idan ta sani zasu samu matsala kuma bana son haka ya fara Haj Karima yanzu haushin Rayhan ta ji "Rayhan ya kike abu kamar baki da wayau, ya zaki ce ba za ki fada masa ba, wannan ai shirme ne" "Nidai Don Allah Aunty ki barni da abin dake cikina kuma ni zan zame masa uwa da uba, ni zan zame masa duk wani farin ciki na nan duniya" Haj Karima ta ce ba za yu ba dole a zubar da cikin nan, wannan ai abin kunya ne wallahi Rayhan ta mike a fusace "me kika ce Aunty? Abin kunya fa kika ce" ta nuna cikin ta da yatsa "wannan cikin ba zan taba zubar dashi ba, zan haife shi kuma ina matukar son abina, sannan akwai sadakin Aliyu a kaina a lokacin daya min ciki, cikina na jerin cikin da aka same su ta hanyar yin aure" Tana gama magana bata jira ta ji me Haj Karima zata ce ba ta yi wucewarta, dakinta ta shiga ta fada kan gado ta fashe da kuka, Haj Karima ta budo kofar ta shigo ta zauna gefen Rayhan "Yi hakuri Rayhan, na yi kuskure da na ce a zubar da abin dake cikinki, bansan ko shine kwanki daya ba a duniya, kila shi zai taimaka miki, kila ya zama abin alfahari a duniya baki daya, Allah ya sauke ki lafiya" Rayhan ta dago ta kalli Haj Karima, rungume ta tayi cikin muryar kuka "amin Aunty ina neman wani alfarma" "Ina sauraranki" "Zan koma London da zama" Haj Karima ta ce meya faru, da kinyi zamanki, ina tare dake Rayhan ta ce Aunty kina samun miji aure zaki yi ki tafi ki barni, kuma ba zan iya zama a wani gida ba saboda na saba zama cikin yenci da isa Haj Karima ta ce Rayhan zan biki mu tafi tare, mahaifinki ya bani amanarki, ba zan taba yarda ki wulakanta ba ko wani abu ya cutar dake Rayhan ta ce yaranki suna bukatarki kisa dake, ki zauna anan abinki Haj Karima ta ce yara suna wajen mahaifinsu yana basu kulawa hakama matarshi tana kula dasu, zamana ya kare a gidan ba komawa zanyi ba, karki manta dani da mahaifiyarki uwar mu daya ubanmu daya dole zan kula dake ko ba'a bani amanarki ba Rayhan ta ce Aunty nagode da kulawarki a gareni, Allah yabar min ke "Amin yata" Mu hadu a page 5 09049493054

Post a Comment

ADS HERE
ADS HERE