ADS HERE
Posts

(JANNAT tsugunno Bata kare ba) PAGE 7

 *⚖️👩‍🎓🎓 JANNAT (tsugunno bata kare ba)🎓👩‍🎓⚖️*


_LABARI DA RUBUTAWA (MRS ABDULL CE✍️)_


*Hakkin mallaka na mrs Abdull ne kawai ban yarda wani ko wata ya juya min labari na ta kowacce siga ba hakan laifi ne mai girma kuma tabbas zan dau mataki, idan suna ko halayya yazo daya akasi ne, labari na kirkirarren labari ne banyi shi dan cin zarafi ko tozarci ga wani ko wata ba, kuma insha Allah zan ringa posting sau hudu ne a sati*



_Littafin SADAUKARWA ne ga mamana *Khadijah sulaiman Gombe* alkairan Allah su tadda ki har gadon bacci_



https://chat.whatsapp.com/HeaWp9GiWRu75eiQOSyung



 *_________________________________*


 *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*

*🇦SSOCIATION🤝🏻*

 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_________________________________*

~SHAFI NA BAKWAI~



*TUKUNYAR KI SIRRIN KI*

``` Sirri na gaba da nake so na gabatar muku shine akan dafa nama mai tauri  kamar ganda haka ko kan sa ko kafaarta, mata da yawa sun san ana iya saka cokalin karfe biyu zuwa uku yakan saka ya nuna da wuri,to wasu matan basu ma sani ba, to ga wani sirri  da nake tafe dashi a Wannan ranan, uwargida amarya da koma wace, idan kin tashi dafa wadanda abubuwan, ganda ,kan sa,kafar sa, da sauransu ki samu paracetamol dinki guda daya ko biyu ki jefa a ciki🤨yes nace paracetamol, wata zata ce paracetamol? To idan kina tantama ki gwada, shiyasa duk macen da bata san sirrin girki ba wallahi tana cikin damuwa. a Matsayin ki na mace ya kamata ace kullum kina binkice ko da sai daya ne a rana akan girke_girke,abinda muke yi ne abinda kuma zai amfane mu, to ya kamata dan Allah mu tashi tsaye domin ganin mun faranta  ran mazajen mu da  daɗaɗan girke girken mu.


______________________________🤳


Bayan gabatar da Shari'a maga takarda ya zauna sannan barrister JANNAT ta Mike kasancewar fahad bashida wani lauya da zai tsaya masa.

Cikin jarumnta irin nata da kaifin basira ta fara maganar kamar haka ''ya mai girma mai Shari'a sunana barrister JANNAT Abdullahi kaltanga, kuma Ni lauya ce mai zaman kanta, ranan Laraba da ta wuce a makarantar gwamnati dake unguwar herwagana anan cikin fadar jahar Gombe , aka tsinci kairat yarinya mai kimanin shekaru 7 a duniya anyi mata fyade an faffasa mata fuska an yadda  ita cikin banɗaki, Wannan abin kuma ya kasance ne daidai lokacin da ita mahaifiyar yarinyar ta je domin kai mata abin da aka umarce su da saya, kasancewar ba'a ga yarinyar ba a aji ya saka kawar ta wato sakina ta fadi wa malamin su taga yarinyar malamin su ya kira ta hanyar banɗaki , wannan dalilin ya saka malamin da kuma ita yarinyar da mahaifiyar yarinyar nufarr hanyar banɗaki, ranki ya dade abin takaici da mamaki shine ganin kairat da sukayi kwance shame shame Bata motsi anyi mata fyade an daure bakin ta da dankwalin makarantar ta, wannan dalilin ya saka su duruwa cikin banɗakin dan gane wa idon su,suna shiga ciki kuwa, shi wanda ya aykata wannan laifin da gudu, amma duk da haka sai da Allah ya nuna masa kaidin sa da zalunci da yayi niyya bazai daure ba, bai san yarinyar da ta gansu tana bakin kofar ba, hakan ya saka shi cin tuntube da ita inda har ya mata targade, wannan dalilin ya saka malamin makaranta Usman da maman kairat kai su asibiti domin duka halin da suke ciki, ya mai girma mai Shari'a ina son kotu ta yi min izini domin fara gabatar da sheda na na farko da zasu tabbatar wa da duniya da kuma wannan kotun cewa wanda ake zargi shi ne ya aykata wannan laifin.''

"Kotu ta baki dama'' Alkali ta fada tana gyara glass din ta.

Shaida ta ta farko itace malamin makaranta Usman idan yana kusa ya matso, JANNAT ta fada tana isowa gaban akwati da ake wa masu bada shaida tanbaya, Usman ya taso ya shigo cikin inda aka tanada domin sa, 

"Malam Usman ko zamu iya sanin cikakken sunan ka?'' JANNAT ta tanbaya cikin salon ta ta kasaita.

''sunana Usman Adamu wanda aka fi sani da zunnu amma a gida ne ake gaya min wannan suna, kuma Ni dan Gombe ne nayi karatu na da komai a Gombe inda yanzu haka na kammala digiri dina nake bautar ƙasa a makarantar gwamnati dake unguwar herwagana cikin nan fadar jiha.''

JANNAT tace ''malam Usman shin mecece alakar ka da wannan Shari'a sannan wacce masaniyar kake da shi game da ita wannan Shari'a?''

"Eh toh kamar yanda kika fada gabatarwa ni malami ne a makarantar su khairat ,bayan mahaifiyar ta ta je ta same ni ne sai muka shiga neman ita yarinyar , to bayan sakina ta kaimu banɗakin muna shiga muka samu ita yarinyar kwance motsin da muka ji a bayan mu shi ya jawo hankalin mu muka juya ganin Mutun ya fita da gudu ya sa muka biyoshi kuma Allah ya nuna mana wanda ya aykata wannan al'amarin,''

''shin wa ka gani ya fita da gudu malam Usman'' JANNAT ta tanbaya

Usman ya gyara tsayuwar yace '' malam Fahad Wanda Kuma shine dama kai tsaye aka zargi wallahi shine ya fito daga banɗakin da gudu bayan mun shiga.''

Girgiza kai JANNAT tayi sannan tace '' ya mai girma mai Shari'a , wannan itace shaida ta ta farko wanda take tabbatar da cewa shi day wannan yaro Fahad shibya aykata wannan ta'adda. Shaida ta ta biyu wacce itace mahaifiyar wannan yarinya da abin ya kasance a kanta , bayan ita kuma inason tanbayan Fahad shun ya aminta shi ya aykata?idan bai yarda ba zan cigaba da kawo shedu wadanda zasu tabbatar shine ya aykata wannan laifin....

Kafin JANNAT ta rufe baki, cikin tijara da kangara Fahad ya bude baki yace ''lawyer nine na aykata sai me? Nayi wa yarinyar fyaɗe a makaranta kuma na amsa laifukan, karshe ina yanke hukunci ne? Ga fili ga mai doki, ki daina wahalar da kanki barrister.''

Fahad ya faɗa yana daga wa JANNAT hannu.

Murmushin da yafi kuka ciwo tayi, way yara gaba daya sun dawo yan iska kowa yana da daurin gindi gani yake babu abinda ya isa ya faru! Yana da damar aykata laifi a duk inda yaso a lokacin da yaso? Baza ta dauki wannan iskancin ba.''

Duk cikin ranta take maimaita wannan zancen.

Rigar dake jikin ta ta gyara sannan tace ''ya mai girma mai Shari'a da wannan katsalandan da kuma gatsali da wannan yaro yayi wa kotu nake rokon kotu ta yanke masa hukunci dai-dai da abinda ya aykata Nagode mai Shari'a.

Tana faɗin haka ta koma ta samu waje ta zauna.

Bayan yan rubuce rubuce Alkali ta ɗago kai ta kare wa kowa kallo sannan ta fara bayani mai kama hankali,  a bisa baya mai da aka samu da shaida da kuma amsa laifi daga bangare kaza zuwa na kaza daga wannan sashin zuwa wancan kotu ta yanke wa Fahad hukuncin zama a gidan yari na tsawon shekaru goma sha biyar tare da taran kudi Naira dubu dari biyar domin bawa yarinyar da ya tozarta sannan kotu tana umarta da a gaggauta mika Fahad gidan yari daga an tashi daga Shari'a.

Tana gama bayanan ta ta buga guduma ta mike kowa ma miƙewar yayi yace kooooot sannan aka fara kacaniya.

Fahad da yake jin ko a jikin sa ya cigaba da kallon yan sanda dake kacaniyar fita dashi daga cikin kotun.

Hajiya laaami dake jin kamar ta haɗiye Zuciya ta mutu sabida bakin ciki da takaici ta matso gaban Fahad tana jin kanta na sarawa kamar ta kashe yan sandan nan haka zuciyar ta ke raya mata , cikin karamar murya da kana ji zaka tabbatar akwai alhini da damuwa cikin ta tace zaka fito Fahad nan ba da jimawa ba , kuma ɗaukar fansa ya riga ya shiga jinina sai na dauki fansa Fahad.

Tana faɗin haka kawai ta juya ta fita shi kuma aka saka shi a mota.

JANNAT da ranta yayi mata kal sabida daɗi ta kama sakina da khairat suka fito ita ma ta shige mota suka tafi fuskar ta dauke da maɗaukakin murmushi.

Kai tsaye gidan maza aka dosa da fahad yana ta raba idanu kamar ya ci kudin ayka.

_NUWAIRAH_

Washe garin da Hajiya laami ta tafi itama safiya tana yi ta wuce, bata bar gidan ba sai da tayi alart na 2million cikin Account dinta, inda suka yi sallama da leemat itama zasu dawo Gombe, kai tsaye Nicon Hilton ta wuce , olready an kama masu daki. Kamar gida haka nuwairah ta maida wannan hotel din dan haka tana zuwa ta nufi masaukin da ya kasance nasu.

Katon parlou ne mai dauke da maka makan kujeru sai tv da kayan flowers kayataccen parlou ne wanda ya ci kuɗi masu yawa, zaka dauka cikin wani gidan kake idan baka san wajen ba. 

Knocking tayi ta ciki aka ce ''yes'' sabida an san da zuwan ta dama.

Turo kofar tayi ta shigo sannan ta miyar ta murɗa key din.

Mutumin da a kalla zaiyyi shekaru sama da hamsin ne ya miƙe ya nufo ta, baki ne kirin mai katon jiki fuskarshi babu alamun gashi ko kadan way na saje, kanshi talll yake kamar gwiwa babu wani gashi, a takaice dai kallon farko kayi wa mutumin nan idan kana cike da hankalin ka kuma baka taɓa yawon duniya ba zai baka tsoro, amma da yake mai abu ne da abinsa , ma'ana nuwairah ta gama sabawa dashi kawia sai ta fada jikin shi shima cikin dariyar sa mai muni ya kyalkyale da dariyar yana hada ta da kirjin shi.

Jawo ta yayi har kan kujera ya zauna sannan ya kalli kyakkayawar fuskarta yace bebe I missed you wallhi, itama wani farr tayi da idanu sannan tace ''i missed you more alaji na''

Wata dariyar ya sake sheke wa dashi sannan ya fara cire mata dan karamin gyalen da ta daure kan ta dashi daga karshe day suka samu masauki a can cikin bedrom din da mashigar kofar sa ke parloun.

_Wanene Alhaji Tukur?_

Alhaji Tukur kasurgumin dan mafia ne wanda baya ɓoye sana'ar sa ko kuma yaji kunyar a sani, kai tsaye shi dan mafiya ne wanda suke da babbar kungiya da sune shuwagabannin ta kuma jiga jigai, ya mallaki dukiya mai tarin yawa, bashida mata kuma bai taɓa haihuwa ba, sai day katon mazinaci ne , babu ruwan shi da salla salati, sadaka ko kuma abinda ya shafi Musulunci kai tsaye dai yana rayuwa ne bai san wanne hakkoki Allah subhanahu wata'ala ya daura mishi a kanshi ba, yana da yara masu matukar yawa da suke masa ayki, daga masu kuka da harkokin sa na kwayoyi da hodar iblis da ake shigo masa dashi daga wasu ƙasashe sai mai kula da gidan rawa da gidan giya, Alhaji Tukur duk anan dukiyar sa take fitowa shahararren, dan iska ne na bugawa a jarida ,sun hadu da nuwairah ne a wani magazine a kasar turawa inda anan suka jone sabida inkiya da suke wa junansu wanda su suka sanshi nan da nan ya gane harkar da take ita ma haka, dan haka ne suka dunkule suka zama tsintsiya madauri ki daya, babban yaron shi musaddiq wanda ya kasance hatsabibi marar imani mara ta ido, shine yake kula masa da harkokin sa na shigo da kwayoyi da hodar iblis cikin Nigeria, an kama musaddiq wanda akayi Shari'a in da barrister JANNAT ta jefa shi gidan yari, shi kuma yana mai ikirarin ganin bayan ta a wannan lokacin (karanta littafin abu a duhu dan jin cikakken labarin hatsaniyar JANNAT da musaddiq) har zuwa wannan lokacin JANNAT bata san musaddiq ya fito daga gidan maza ba sabida bata da labarin kuma bai nuna mata wata alama da zata tabbatar da hakan ba, yanzu haka gobe yake shirin durowa Nigeria sabida aika da Alhaji Tukur yayi masa na makamai da bindigogi domin ajiye a gidan da suke ajiye mutane domin yankawa. Wannan KENAN.

*Washe gari*

Karfe 7 na yamma nuwairah da Alhaji Tukur suka je taran babban yaron Alhaji Tukur wato musaddiq a airport jirgin su na sauka fasinja suka firfito shine na karshen fitowa sanye da rigar sanyi ruwan zuma da bakin wando ,matashin saurayi ne da a kalla zaiyyi 35 fari ne kall kuma bashida wani tsayi.

Har gaban Alhaji Tukur yazo suka hau gaisawa da juna. Nan motar da ta kawo su ta debe su sai Nicon otel.

Dakin da aka kama domin musaddiq nan ya shiga ya yi wanka ya shirya tsaf sannan ya fito ya samu ogaan shi da dadiron shi a masaukin su.

Zana yayi kujerar dake gefe yana nade hannun rigar shi mai anini.

Cikin murmushi Alhaji Tukur yace '' dafatan yanda nake bukatar komai , abubuwa sun tafi lafiya?''

Shima cikin murmushin yace everything is going to be well zuwa yanzu hankulan mu bazasu kwanta ba sai Rasheeda ta iso da kayan da muka siya sati mai zuwa cikin kwanciyar hankali daga sannan ne zamu iya fahimtar komai ya tafi yanda ake so ko akasin haka.'' 

Girgiza kai Alhaji Tukur yayi sannan yace ''olrite sai ta iso din domin Rasheeda a ƙalla zamu iya cewa tasan aykin ta sosia.'' Shima girgiza kai yayi yace '' idan kayan suka iso zamu iya daura aykin mu daga inda muka tsaya tunda yanzu mun gama naka ko boss? Kaya kawai muke jira su iso.'' musaddiq  yayi Maganar yana kallon Alhaji Tukur.

Shima Alhaji Tukur din kallon sa yayi sannan yace '' nikam a ganina kuma a hasashen da nayi da kun bar maganar yarinyar nan shi ne zai zama mafi alkairi a wajen ku, ba wai zan kwarzan ta ta bane a'a gaba dayan mu yan gari gudaa ne me kuke nema wanda baku samu ba shin ta san daku ne ma zuwa yanzu, rasheda kawai take nema kuma ba lallai ta same t nan kusa ba, duk da kuwa tana shiga gomben ta fita bana tunanin zata iya haduwa da ita, kaga kuwa barin ta shine mafi alkairi a tattare daku tunda kai kam zuwa yanzu ta ma manta da kai kuma bata san baka gidan maza ba.

Yar dariya musaddiq yayi sannan yace '' JANNAT! JANNAT!! JANNAT!! Duk yanda kake tunanin barrister JANNAT ta wuce nan bos hatsabibiya ce ta gaske kan ta yana ayki tamkar na'ura mai ƙwaƙwalwa, idan ban dauki mataki a kan ta ba hankali na bazia kwanta ba, kuma har yau tana neman Rasheeda ido rufe kuwa , tonon asirin Rasheeda kuma kamar namu asirin ne saboda komai tare muke yi da ita dole mu dau mataki kan barrister JANN....!

Kafin musaddiq ya karisa nuwairah ta taso ta dawo tsakiyan su ta zauna tace '' alaji na sai naji kamar JANNAT kuke fada waya barrister JANNAT kaltanga ko kuwa? Me hadin ku da makiyiya ta? Nuwairah ta fada tana zare ido da neman alamun karin bayani domin sun soso mata inda ke mata ƙai_ƙayi.✍️


Kana bukatar albarka? 

Yawaita salati ga Annabi (S.A.W).



Littafin JANNAT (tsugunno bata kare ba) littafin kudi ne game buƙatar karanta wannan littafin daga farko har karshe zata biya kudin ta Naira dari uku cas ta wannan account din 0009243783 Nafisa Rabiu Umar jaiz bank, sai a turo shaidar biya ma'ana Screenshot KENAN ta waanda suka shirya har na fara jin alert, idan na gama free PAGES bazan tsaya ba zan cigaba ne da posting kawai.


_Garabasa! Garabasa!!_


*JANNAT⚖️👩‍🎓🎓(TSUGUNNO BATA ƘARE BA)*

          NA

_MRS ABDULL_


*ABU BILAL!!!*

    

 _MAJIDAƊI_


07059305867,07033636337


*AMINCIN ALLAH YA TABBATA A GAREKU MASOYA FITATTAUN MARUBUTAN NAN YAYA DA ƘANWA, WATO NAFEESAT RABI'U UMAR DA ƘANWARTA MARYAM ISMAIL MAJIDAƊI(JORDERH), SHIN KO KUN TUNA SU?, SUNE DAI MAMALLAKAN LITTAFAN NAN DA SUKA REWAƊE MEDIA BAKI ƊAYA WANDA SUKAI AMSA KUWWAR KARAƊE KUNNUWANKU MRS ABDUL ƊIN NAN DAI TAKU MAI MUGUN DUHU MARUBUCIYAR JANNAT, MARYAM MAJIDAƊI MARUBUCIYAR LITTAFAN NAN NAKU WATAU HANAN,RUHIN FANSA,SHI NE AJALINA DA SAURANSU*


*KADA DAI NA CIKAKU DA SURUTU KU MATSO KUJI KU KARKAƊE KUNNUWANKU, KUJI YAU DA ME SUKA ZO KUN DAI SAN KOMAI SUNA YINE DAN NISHAƊANTAR DAKU DA FAƊAKAR DAKU, TABBAS BA ZAKUYI DANA SANI BA KU MATSO KUJI A YAU MA SUN YUNƘURA SUN TATTARO BASIRA SUNYI TUNANI MAI KYAU WURIN SUN ƘAYATAR DA KU A CIKIN DAƊAƊAN LITTAFANSU WATO JANNAT(TSUGUNNO BATA ƘARE BA) CI GABAN JANNAT NA NAFISA RABI'U UMAR ,IN DA MARYAM ISMAIL KUMA TA ZO MAKU DA WANI SABON LITTAFIN TA MAI SUNA ABU BILAL!!!, KAI DAGA JIN SUNAYEN KASAN ZA'A SHA KALLO DA TAƘADDAMA A CIKI TABBAS BAZAKUYI DANA SANIN SIYAN LITTAFAN NAN BA,KUƊIN LITTAFIN A NAIRA ƊARI UKKU KACAL(300) NORMAL GROUP KENAN,WANDA KESON DUKA BIYUN KUMA ZAI BIYA NAIRA ƊARI BIYAR(500)NORMAL GROUP KENAN,VIP KUMA KO WANNE XAKA BIYA NAIRA ƊARI BIYAR(500)EACH ONE. WANDA MANYAN HAJIYOYI MASOYAN MU KUMA NASAN KO 1K AKA CE BAZATA GAGARA BA, AHTO MEYE KUMA WANI 1K ALLAH NA TUBA IN DA BIYAN BUƘATA😂*


*DOMIN ƘARIN BAYANI ZAKU IYA TUNTUƁAR LAMBOBI KAMAR HAKA*

07059305867,07033636337


MASOYA A KO INA MUNA ALFAHARI DA KU SAI KUN ZO


zaki iya biyan kuɗi a wannan account ɗin 2152592149 maryam ismail UBA bank ko ta wannan account din 0009243783 Nafisa Rabiu Umar jaiz bank. shaidan biya ta waɗan nan lambobin dake sama.




*Girke girken zamani* 

Girkin mu na yau shine👇





 *MIYAR HANTA.* 🥣



*Abubuwan buk'ata.*


Hanta rabin kilo

Attaruhu 4

Tattasai 3

Albasa 2

Maggi 5

Gishiri

Citta 3

Tafarn


uwa 2

Kori (Curry)

Onga

Man girki.


*Yanda zaki had'a.*


 Da farko dai uwar gida zaki wanke hantar ki yanka dai² misali,sai ki sa a tukunyarki ki yanka mata albasa,sannan ki kawo kayan maggi ki sa k'waya d'aya da d'an gishiri,idan yayi sai ki sauke ki kwashe a wani kwano,sai ki zuba mai da kayan miyanki ki soya ya soyu da kyau,idan ya soyu sai ki zuba ruwa kad'an ki sa hantar ki kawo maggi,gishiri,citta,tafarnuwa,da kori ki sanya,sai ki barshi kamar minti sha biyar zaki ji gida ya d'au k'amshi sai ki sauke,miyanki yayi kenan.


 Ita dai wannan miyar zaki iya cinta da shinkafa ko sakwara.

 A ci dadi lafiya.😋😋




#share 

#comment

#Vote

Pls 

Dan girman Allah duk wacce ta karanta tayi share sabida Allah



*MRS ABDULL CE*✍️

Post a Comment

ADS HERE
ADS HERE