ADS HERE
Posts

JANNAT (tsugunno bata ƙare ba) page 4 daga alƙalamin MRS ABDULL

 




*⚖️👩‍🎓🎓 JANNAT (tsugunno bata kare ba)🎓👩‍🎓⚖️*

_LABARI DA RUBUTAWA (MRS ABDULL CE✍️)_

*Hakkin mallaka na mrs Abdull ne kawai ban yarda wani ko wata ya juya min labari na ta kowacce siga ba hakan laifi ne mai girma kuma tabbas zan dau mataki, idan suna ko halayya yazo daya akasi ne, labari na kirkirarren labari ne banyi shi dan cin zarafi ko tozarci ga wani ko wata ba, kuma insha Allah zan ringa posting sau hudu ne a sati*


_Littafin SADAUKARWA ne ga mamana *Khadijah sulaiman Gombe* alkairan Allah su tadda ki har gadon bacci_

 *_________________________________*

 *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_________________________________*


*Kasan addinin ka*

```LOKUTA HUDU NA AMSA ADDU'A```

           Da Sunan Allah Mai Rahma Mai Jin ƙai


4. LOKACIN DA BAWA YA DAGA HANNU SAMA YAYIN ADDU'A: Yana Daga Cikin Ladubban Addu'a Bawa Ya daga Hannunsa Sama Yana Mai Kaskantar da Kansa Sannan Ya Roki  Ubangiji Bukatunsa. Hadisi Ya Tabbata Manzon Allah (ﷺ) Yana Cewa:

ﻋﻦ ﺳﻠﻤﺎﻥ ﺍﻟﻔﺎﺭﺳﻲ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﺃﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ: ”ﺇِﻥَّ ﺭَﺑَّﻜُﻢْ ﺗَﺒَﺎﺭَﻙَ ﻭَﺗَﻌَﺎﻟَﻰ ﺣَﻴِﻲٌّ ﻛَﺮِﻳﻢٌ، ﻳَﺴْﺘَﺤْﻴِﻲ ﻣِﻦْ ﻋَﺒْﺪِﻩِ ﺇِﺫَﺍ ﺭَﻓَﻊَ ﻳَﺪَﻳْﻪِ ﺇِﻟَﻴْﻪِ، ﺃَﻥْ ﻳَﺮُﺩَّﻫُﻤَﺎ ﺻِﻔْﺮًﺍ“
{ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ: ١٤٨٨}

An Kar6o Daga Salmanul Farisy (ra) Yace: Lallai Manzon Allah (ﷺ) Yace: “Lallai Ubangijinku Mai Kunya ne Kuma Mai Karamci, Yana Jin Kunyar Bawansa Ya Daga Hannu Zuwa (Ya Roqeshi)Gareshi Ya Sauke Hannun ba Tare da Ya Biya Masa Bukatunsa ba”.
{Abu-Daud:1488}

______________________________🤳

~SHAFI NA HUDU~

*_Daga wannan shafin in Allah ya yarda zamu bar bangaren addini mu koma na girke girke shima zamuyi shafi hudu ina baku kalolin girke da ya dace sannan mu koma bangaren gyaran jiki in Allah ya yarda. Wacce take buƙatar sharawa dangane da girkin da ya kamata a bayar zata iya baje kolin shawarar ta ta wannan number Sallama kawai sai kice ga girkin da kike bukata a ya kasance a shafi na gaba_*
 _07059305857_



Jirgin su bai tsaya a ko ina ba sai filin tashi da sauka na jiragen sama dake abuja Nmdi azikwe.  suna fitowa a jirgi babbar matar wacce itace shugabar tafiyar ta ciro waya tayi kira ana dauka cikin isa tace
'' Isma'il ka kama dakunan da na sanar maka kuwa?'' bansan me aka fadi ba daga dayan bangaren, can kuma tace ''maganar banza kenan, ya za'a yi sai da na dauko mutane kuma kace baka kama dakuna ba?'' sai kuma tayi shiru can tace '' gaskiya banison wani otel idan ba Nicon Hilton ba ya fi sirri sannan kuma da can na saba, kana ina ne yanzu? Ok tohm mu hadu karamin gidan Alhaji dake kan titin zuwa airport yanzu ka bani makullai.''
Tana faɗin haka ta kashe waya ''tace dan Allah kuyi hakuri wallahi yayi min shirme ne bari kawai mu wuce gidan deputy nasan can ma Babu wata matsala.'' dukkansu amsawa suka yi da ''ok babu komai'' sannan suka dan fara tafiya, sun kusa fitowa daga airport din sai ga motar da tazo daukan su, motoci ne guda biyu masu rai d nunfashi ko kara baka ji idan suna tafiya sabida tsabar sabunta da kyau, duk suka ɗuru cikin motar aka lulaa dasu.
Kai tsaye wani hadadden gida suka nufa bayan horn mai gadi ya wangale gate drivers suka danna kai cikin gidan, bayan parcking kowa ya fito kayan da suka zo dashi kaf a wajen suka barsu da alama za'a shiga musu dashi ne, ko minti biyu basu yi da sauka ba sai ga mota ta shigo gidan ,da alama wanda suka yi magana dazu ne yazo yana fitowa daga motar ya taho wajensu gaida su yayi duka, dai-dai ku ne a cikin su suka amsa sannan ya kalli matar yace ''wallahi Hajiya matsala aka samu na manta ko kadan ban sanar miki ba, nicon suna gyara daga bedrom dinsu zuwa sauran abubuwa shine dalili kuma Alhaji ya saka Ni ayki a Company ban samu na kira ki na sanar miki ba dafatan Zaki gafarce ni.'' 
''bakomai '' kawai Hajiya tace sannan ta mika masa hannu.
Daga aljihun sa ya ciro keys da waya ya mika mata, hannu ta sa ta karba shi kuma ya juya ya shiga mota.
Yana mamakin hali irin na Hajiya Madina kwata kwata kamar wata karya babu kamun kai ko kadan irin na mata a tattare da ita, ko kadan Alhaji saada bai san mai take aikatawa ba, itace kawo maza ita ce kawo mata kowa nata ne ,da wannan tunanin ya shiga mota yaja ya fice daga gidan.
Hajiya Madina da ta karbi makullai kawai sai tayi gaba, su nuwairah na biye da ita har cikin parloun gidan, dakuna ne da akalla zasuyi biyar cikin parloun sai wata hanya da alama zata sada mutum da kicin ne na parloun, kujeru ne masu taushi ajiye a parloun dan haka duk duka zube a kai, kowa tana fadin 'wash.'' nuwairah ne da gajiya da sha'awa suka lullube ta ta kalli Hajiya Madina tace '' Hajiya I need to rest'' cikin fara'a Hajiya Madina tace ''ok dear barin baki key ga daki, go and bath Zaki jini anjima kadan.'' da ''ok'' nuwairah ta ansa Sannnan ta Mike ta amshi makullin ta wuce tana karkada boobs da mazaunai. Gaba-daya da kallo suka bita musamman wacce tun a airport take ta shige wa nuwairah, nuwairah na wuce wa matar ta juyo tace, '' Madina nawa ne farashin yarinyar nan?''
Dariya Madina tayi sannan tace na kwana nawa laami?'' 
''duka kwanakin'' wacce aka kira da lami tayi maganar kamar zata hadiye Hajiya Madina.
''Ok 1.5 million ta fada tana daga gira'' 
"Na saya wallahi inday da gaske din nan yanda take a zahiri idan an shiga daki ma haka take zan bada 2million yayi ko?''
Dariya wacce aka kira Madina ta kwashe dashi sannan tace yayi asha romo lafiya'' ta faɗa tana kallon sauran .
Laami bata ce komai ba ta tashi ta wuce dakin da nuwairah ta shiga, karar ruwa da taji a banɗaki ya tabbatar mata wanka take dan haka ta shiga tuɓe nata tufafin, sai da tayi zigidir haihuwar uwarta sannan tabi nuwairah toilet din.
Nuwairah dake murza soso a jikin ta wanda yaji kumfa busbus sabulun sai kamshi yake, wanka take cikin salo kamar wani na ganin ta, laami dake tsaye bakin kofar toilet kusan shide wa tayi da ganin halittar nuwairah, ''lallai a bin da gaske ne'' ta fada cikin ranta.
Alamun kallo da nuwairah taji a jikin ta ya sakata hanzarin kunna shawa ta wanke fuskarta sannan ta juyo, Hajiya laami ta gani tsaye bakin kofa kamar kuma yadda tayi hasashen haka ta ganta wato yanda take son ganin nata, ɗan murmushi ta sake sannan tace ''welcome'' dan matar ta mata sosia a iya tsufan ta bazaka ce tana da wannan halittar ba sabida bata yi wani sake wa duka ba. Itama laamin murmushi tayi sannan ta fara bada step tana nufo nuwairah. (Wa'iyazubillah abinda de kake tunanin mata da miji ne kawai zasu iya yi amma yanzu abin ya zarce hankali matan ma aykata shi suke, Allah ka sa mu cika da imani)
Kusan minti talatin a banɗaki sannan suka fito, manne da juna suna ta dariya kamar hauka sabon kamu. A bakin gado suka zauna nuwairah tace ''Hajiya baza ki iya dani ba ke kadai ban taɓa yi ba ban kuma san ya za'a yi na satisfying ba, dake ke kadai inaaa bana ganin zaiyyi wu, gaskiya a kira leemat.'' 
Dan murmushi Hajiya laami tayi sannan tace ''Duk yanda kike ji da duk wata sha'awa ni laami na dama ki na shanye dan haka bamu bukatar kari na yi cinikin ki har na biya Kada ki damu.''
Itama nuwairah murmushi tayi tace ''Tabbas idan ban wuce ki ba lallai bazaki wuce Ni ba sai dai muzo dayday.''
Da wannan musayar kalamai a bakin su suka shiga aykata alfasha(Allah ka tsare mana imaninmu)
_JANNAT_ 
Cikin wadannan kwanakin gaba daya shirye_shiryen jarabawa yara suke domin za'a fara jarabawa , karatu suke sosai babu kama kafar yaro dan ba baya suke ba kowanne a cikin su yakan zo na daya ko na biyu ne a cikin ajinsu, da da akwai zero ma za'a basu ba na daya ba sabida yanda suke kwashe karatun Musamman nasmah ita kamar ma diban karatun ake ana zuba mata shi cikin kayin ta, suna ta shirye shirye sosai da sun gama jarabawa kuma zasu wuce kaltanga domin gaba daya acan suke hutun su duka.
JANNAT kuwa tana zuwa aykin ta bangare guda kuma tana cigaba da binkice a kan Rasheeda sannan kullum tana cikin taka tsantsan ta inda nuwairah zata bullo mata, domin tun ranan da taga sakon ta da Number Nigeria har yau bata sake Turo mata wani sako ba, kai tsaye office ta wuce lokacin 2 na rana, bata da Shari'a kawai dai akwia wasu ayyuka da take son karasawa Dan haka tana shiga su ta fara yi.
Bata fi mintuna talatin da zama ba aka nemi izinin shigowa dan haka ta bada izini, mace ce da a kalla zata yi shekaru 35 mai matsakaicin jiki guntuwa yar baka haka, da ka ganta zaka san bata cikin hankalin ta ko natsuwar ta ko kadan, gyara zama JANNAT tayi tana fuskantar ta sannan tace ''zauna'' tayi mata nuni da kujerar dake gaban teburin ta.
Zama matar tayi sannan tace ''ina wuni ranki ya dade ya aiki?'' lafiya'' JANNAT tace sannan ta rufe littafin dake gaban ta tace ''meke tafe dake yayata? Matar Tana jin haka ta tabbatar da abinda ake gaya mata kan JANNAT babu karya ko wasa a ciki, bata taɓa zato ko tsammanin zata samu irin wannan tarba daga lauyar ba dan haka sai ta saki jiki ta gyara zama.
'' baiwar Allah taimako nazo nema dan Allah dan alfarmar Annabi Muhammadu ki taimake Ni ki bi min kadu na kibi mana hakkin mu dan Allah. Ta faɗa hawayen dake tare a idon ta Yana silalowa.
JANNAT da wani abu yazo ya tsaya mata a rai, a hankali idon ta suka fara canza kala, tasan duk abinda zai saka mace kuka har ya kawo ta wajen lauya ba abu  bane mai sauki, tabbas matar ta bata tausayi tun ma kafin ta fadi mata dalilin kukan nata, a hankali ta haɗiye abinda ya tsaya mata a makoshi sannan tace ''yayata jeki kan asalin abinda ya saki zuwa guri na saboda na zaku naji ko menene.''
Cikin shasshekar kuka matar ''tace ƴata akayi wa fyade mai shekaru bakwai.''
Wani abu mai kama da narkakken dalma ne ya kwararowa JANNAT a kirji ta tabbatar abinda ke makoshin ta ne ya samu fashewa har ya faɗa zuwa kirjin ta, sai da ta raya hakan cikin ranta domin abubuwa kalilan masu kuma girma su zasu saka mace kamar wannan kuka na farko matsalar miji na biyu ayiwa yarka fyade, tunda ta shigo take addu'ar Allah yasa ba fyaden bane , amma sai aka samu akasi shine. Ta maimaita maganar matar cikin ranta ''yata akayi wa fyade mai shekaru bakwai''. Dan haka ta rintse ido da karfi, yanzu abinda innar ta taji lokacin da ak yi mata fyade tana da shekaru bakwai kenan shine abinda matar nan ke ji?'' ta tanbayi kanta.
A hankali ta ɗago idon ta da suka yi jawur sabida bakin ciki da ɓacin rai tace '' yaushe hakan ya faru sannan a ina?'' tayi tanbayar Muryar ta na sarkewa.
Cikin goge hawaye matar ''tace yata daya wanda mahaifin ta ya rasu ya barni da ita tun tana zanin goyo,nima dama mahaifina ya rasu sai mahaifiyata da nayi aure na bari ,itama kuma bayan mijina ya rasu ba jimawa Allah ya karbi rayuwar ta, dan haka na cigaba da zama da ƴata a gidanmu daga Ni sai masu haya wanda na saka a dayan dakin mata da miji ne sai nake karban kudin Haya nake bukatun yau da kullum, a duk duniya banida wani buri da ya wuce naga yata ta samu ingantaccen ilimi da sani da kuma tarbiyya,dan haka na tashi Tukuru na saka ta a makarantar boko da islamiyya, yarinyar akwia kaifin basira dan haka kowa ke son ta cikin makarantar banida halin makarantar kudi sai na saka ta a ta gwamnati. Rana ta farko tun shigar su aji 2 tazo min da labarin wani malami da aka kawo musu yana da kirki sosai kasancewar ta mai wayo kuma ta iya magana, sai nake ce mata to a girmama mallamai dai sai a samu karatu mai albarka, bamu sake wata magana da ita ba a kan haka, sai ranan da tace min ance su sayi cabort paper a makarantar su to kuma ranan ban tashi da kudi ba nace ta tafi makarantar idan na tashi zan kawo mata, wallahi ranki ya dade ba musu yarinyar ta tafi Ni kuma sai na wuce shagon saida litattafai, naje na saya mata sai na dawo gida sai da na gama komai nawa sai na shirya na wuce makarantar, ina zuwa an fita musu wasa sai na jira sabida bansan ta ina zan neme ta ba cikin dubban jama'a, Kasancewar makarantar Gwamnati akwia dalibai da yawa, bayan an koma aji sai na wuce ajin su kai tsye malamin da ke ciki na tambaya nazo wajen kairat malamin da bazai wuce shekaru ashirin da daya ba. sai yace ay kuwa kairat bata dawo ba daga tara, nace masa ga abinda na kawo mata nan tace za'a zane su idan basu saya ba , kawia sai yayi dariya yace kairat kenan Sarkin tsoro ay nine malamin da na ce su saya sabida zan koya masu wani zane ,dariya nayi na bashi abin zan juyaa akan ko ta tsaya wani fitsari ne ko wani abu, haka kawai naji zuciya ta bata aminta ba da abin sai na tsaya , mutumin mai fara'a sai yace maman khairat barin tanbayi yan aji ko wani ya ganta, haka kawai naji jiki na babu dadi a haka dai nayi masa yaƙe nace to, ina jinshi daga cikin aji yana tanbayar yara dake kusa da inda khairat ke zama ina khairat bilyamin, daga cikin ajin naji wata yarinya mai zaƙin murya tana fadin ''uncle Fahad ya kirata.'' Gaba na ne ya fadi dummm a tare kuma hawaye ya silalo cikin ido na sabida haka kawia naji wani tsoro na ban mamaki ya lullube Ni, malamin ne yace malam fahad kuma? ''Ke sakina ina kika ga sunyi zo nan.'' malamin ya faɗa yana nuna wacce tayi maganar . ''Ranki ya dade wallahi gagara daga kafata nayi a wajen sabida jikina rawa kawia yake yi.'' sai da malamin da naji suna kira Usman yace maman khairat bari mu duba khairat din, bai jira abinda zance ba yayi gaba ,sai da suka yi nisa sannan na dawo hayyaci na, da gudu na bisu kasancewar na daina jin komai kamar wanda aljannu suka shafa, hanyar bandakin makarantar muka yi , inda yarinyar ta kaimu har bakin bandakin sannan tace ''wallahi ina gani ya saka ta a nan mu kuma ya Kore mu shine bai sani ba na leƙo a hankali saboda naga khairat na kuka kuma tace bata so yace sai ta shiga ,kawia da naji an kada komawa aji, shine na koma aji.'' 
Salati kawia na kama ina kuka shi kuma malamin ya shiga buga kofar bandakin, abinda muka gani shi ya rusa duk wani tunani dake kai na , khairat ce kwance an daure bakin ta da dankwalin kanta fuskar ta duk yaguni ranki ya dade jikin ta babu wando😭 matar tana kawowa nan sai ta fashe da azababben kuka.
JANNAT da kuka ya ƙafe a idonta sai canza kala da idon suka yi har wani maroon maroon suke sabida ɓacin rai ,hankacif ta dauka ta share zufan dake goshin ta sannan tace ''sai aka yi yaya''.
Cikin karyayyiyar murya matar tace ''sai kawai muka fada cikin banɗakin muna salati nida malamin yarinyar kuma tana tsaye waje , sai da muka shiga har cikin banɗakin kan khairat kawai muka ga fitar mutum da gudu wani kwallo yayi da yarinyar wajen sabida baisan da tsayuwar ta ba a wajen, malamin da naji yara suna kira Usman shi ya juya da gudu ya bishi yana faɗin ''fahad ne gashi can ya gudu shine.'' usman ya faɗa kamar wani zaucacce , ita kuma yarinyar da ya hankade ta fadi ta saki kuka da alama ya karya ta ko ya mata targade. Ciccibar khairat Usman yayi ya fito da ita Ni kuma na dauki yarinyar mutane dake ihu muka tafi asibiti bamu bi takan kowa dake makarantar ba , bayan munje aka ce sai munzo da yan sanda amma zasu karbe ta ,suka karbe ta da ita da sakina shi kuma Usman ya tafi kiran polisawa, bayan dawowar su ne kuma aka shiga binkice da menene menene ranki ya dade farkon abin kamar za'a yi abin kirki, amma daga karshe da muka je makaranta sai shugaban makaranta yace baisan abu ya faru ba kuma ba'a gaya masa ba ,haka suka yi ta kwana kwana kuma shi malamin ya cigaba da zuwa makarantar babu abinda akayi mishi, shi day wannan malamin su Usman shine mai kula da komai dake tafiya, yanzu haka khairat ta samu sauki sai raunuka da abinda baza'a rasa ba , amma ba'a bi mata kadi ba, shine na tafi wajen wasu polisawan ina zuwa aka hada Ni da babbansu a wajen naji suna kiranshi mudassir, shine yayi min kwatancen nan yace nazo wajen ki zai saka a kamo masa fahad. Matar ta karisa maganar tana kifa kanta akan teburin dake gaban JANNAT tana kuka kamar ranta zai fice.
JANNAT da bata iya furta komai ba sai waya da ta dauka, kira tayi ana dauka tace kun kamo shi? A dayan ɓangaren aka ce ''yes Madam'' 
tace ''ku kulle shi mudassir ka tura zancen kotu jibi zamu shiga Shari'a bana son bata lokaci. ''cikin girmamawa mudassir yace ''insha Allah yaya JANNAT yanzu kuwa'' bata ce komai ba ta katse wayar kawai.
Matar dake kuka ta fara jera godiya kamar zata ari baki tana kuka tana godiya, JANNAT da ta gagara cewa komai ,kawai rufe komai tayi tace kaini naga  yarinyar.✍️


Bana alfahari kuma bana takama, sannan bana jin kaina Ni wata ce ko kuma nafi kowa , sai day nasan cewa alƙalami na baya rubuta shirme✍️ba lallai kuga alƙalami na yana rubuta soyayya ba,kamar na wasu marubutan a'a, ba kullum ne ake kwana a gado ba , ma'ana shine dole rayuwa taɓa kiɗi ne taɓa karatu, babu karya a Alƙalami na ina rubuta gaskiyar abinda ke faruwa ne cikin al'umma, hakan ba Lallai yayi wa makaranta da yawa dadi ko suji suna son karanta littafin ba amma tabbas nasan idan ka karanta sai ka Karu domin a kullum ina fada  alƙalamin *MRS ABDULL* baya rubuta shirme.


Kana bukatar farin jini?
Ka guji cin amana😁


 Kafcen ba a haka zai tsaya ba kamar yanda kuka gani a sama zaku ga wani note basai na gaya maku na menene ba wacce ta karanta ta sani, to haka littafin zai cigaba da zuwa muku da abubuwa irin na gyaran jiki da kuma gyara aure da gyara sanwa da kuma gyara muhalli gyaran Addini yanda mutum zai kyautata tsarkin sa da kuma kyautata ibadar sa duk a cikin wannan littafi na JANNAT (tsugunno bata kare ba)

Littafin JANNAT littafin kudi ne game buƙatar karanta wannan littafin daga farko har karshe zata biya kudin ta Naira dari biyu cas ta wannan account din 0009243783 Nafisa Rabiu Umar jaiz bank, sai a turo shaidar biya ma'ana Screenshot KENAN ta wannan lambar 07059305867 ko katin waya na MTN ta wannan lambar 07059305867 hoton katin za'a turo, free PAGES zasu kare ne da nayi page ashirin cif insha Allah. Na fada JANNAT (tsugunno bata kare ba) na kudi ne kar wata ta gaya min maganar wofi idan na gama free PAGES Dan bazan dauka ba a kiyaye. Mai bukatar biya zai iya biya tun daga yanzu domin wanda suka shirya har na fara jin alert, idan na gama free PAGES bazan tsaya ba zan cigaba ne da posting kawai.

#share 
#comment
#Vote
Pls 
Dan girman Allah duk wacce ta karanta tayi share sabida Allah


*MRS ABDULL CE*✍️


Post a Comment

ADS HERE
ADS HERE