ADS HERE

JANNAT (tsugunno bata kare ba)


 *⚖️👩‍🎓🎓 JANNAT (tsugunno bata kare ba)🎓👩‍🎓⚖️*


_LABARI DA RUBUTAWA (MRS ABDULL CE✍️)_


*Hakkin mallaka na mrs Abdull ne kawai ban yarda wani ko wata ya juya min labari na ta kowacce siga ba hakan laifi ne mai girma kuma tabbas zan dau mataki, idan suna ko halayya yazo daya akasi ne, labari na kirkirarren labari ne banyi shi dan cin zarafi ko tozarci ga wani ko wata ba, kuma insha Allah zan ringa posting sau hudu ne a sati*



_Littafin SADAUKARWA ne ga mamana *Khadijah sulaiman Gombe* alkairan Allah su tadda ki har gadon bacci_


 *_________________________________*


 *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*

*🇦SSOCIATION🤝🏻*

 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_________________________________*



*Kasan addinin ka*


```LOKUTA HUDU NA AMSA ADDU'A```


           Da Sunan Allah Mai Rahma Mai Jin ƙai


1. YAYIN DA AKE KIRAN SALLAH:

 Lokacin da Ladan Yake Cikin Kiran Sallah Shima Lokaci Ne na Amsa Addu'a. Manzon Allah (ﷺ) Yana Cewa a Cikin Ingantaccen Hadisinsa:


ﻋﻦ ﺳﻬْﻞِ ﺑﻦِ ﺳﻌﺪ ﻗَﺎﻝَ : ﻗَﺎﻝَ ﺭﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﷺ : ‏”ﺍﺛِﻨَﺘﺎﻥِ ﻻَ ﺗُﺮَﺩَّﺍﻥِ، ﺃﻭْ ﻗَﻠَّﻤَﺎ ﺗُﺮﺩَّﺍﻥِ : ﺍﻟﺪُّﻋَﺎﺀُ ﻋِﻨْﺪ ﺍﻟﻨِّﺪَﺍﺀِ ﻭﻋِﻨﺪ ﺍﻟﺒﺄْﺱِ ﺣِﻴﻦَ ﻳُﻠْﺤِﻢُ ﺑَﻌْﻀُﻬُﻢ ﺑَﻌﻀًﺎ“

{ﺭﻭﺍﻩ ﺃﺑُﻮ ﺩَﺍﻭُﺩَ: ٣٠٧٩}


An Kar6o Daga Sahli bn Sa'ad (ra) Yace: Manzon Allah (ﷺ) Yace: “Addu'oi Biyu Ba'a Mayar Dasu: Addu'a Yayin Kiran Sallah, da Kuma Addu'a a Fagen Fama Lokacin da Mayaka Sukayi Sahu Suna Kimtsawa”.

{Abu-Daud: 3079}



__________________________📲


~SHAFI NA DAYA~



Ƙaton gida ne wanda daga gate din gidan kawai abin kallo ne,farin fenti ke jikin gate din mai dauke da ratsin purple, gate din mai irin kwalliya da zanen karafuna ne a jiki, daga harabar gidan zaka gane mazauna gidan ko mamallaka wajen suna son Abu fari ko wanda ya danganci farin, fentin gidan fari ne mai dauke da ratsin purple din kamar yanda gate ɗin gidan yake, masu gadi ne guda biyu sanye da uniform na yan sanda a jikin su, kai kawo kawai suke a bakin gate din wannan ya juya nan wannan ya juya nan,can wani bangare daga cikin makeken filin motoci ne manya manya yan yayi masu nunfashi a fake a cikin wata rumfa ita ma ta zamani ce,shukoki ne a shusshuke a kowanne sassa na cikin gidan wanda babu datti ko wani kura a kansu da alama suna samun kula yadda ya kamata. inda asalin ginin da zai sada ka da cikin gidan yake harabar filin, Shashi biyu ne a tangamemen filin wanda dayan yake acan gefe. 

Sashi na farkon na nufa, corridor ce da madaidaicin ƙofa mai matukar kyuau da ka shiga kofar wawakeken falo ne wanda ke ta tashin kamshi, falo ne mai dauke da kujeru leda sit irin masu bukatar sanyin nan, babu wani tarkacen cikin falon sai tangamemen tibi da ya kusa cinye bango yana ta magana a tashar sunna tv , yaro ne mai Kimanin shekaru 14 zaune kan daya daga cikin kujeru,fari ne tas har wata yellow da dauke idanu yake laptop yake dannawa hankalin shi kwance da alama ya iya sarrafa ta yanda ya kamata, dayan kujerar yara be guda biyu duka mata daya zata yi shekaru 11 sai dayar kuma zata yi 8 Yes,babbar ita ke koyawa karamar karatu cikin text book ita kuma karamar tana rubutawa,   dukkansu bakake ne wuluk sai day babbar tafi ƙaramar baƙi bazaka ce sun hada wata alaƙa ta jini da wannan yaron ba, sai ka tsaya ka dube su sosia kaga kamar amma itama kamar jini ce, cikin rashin son magana babbar tace "Wallahi nasreen na gaji wanne irin abu ne haka ki rubuta market kawai kin gagara kin maida hankalin ki kan kallo zan daina koya miki wallahi na fada miki yaya juniour ka gaya mata wallahi'' tayi maganar tana kallon wanda ke danna Computer.

"Ok na gaya mata ko nasmah Ni zan gaya mata? Tun farko wa ya saka ki kunna tv ba taurin kai bane kinsan nasreen da kallo yaushe zaku iya karatu kuma kuna kallon tv? Idan kina so ta gane abinda kike koya mata kashe kallon zaki yi tukun sannan idan kun gama ki kunna.'' yayi maganar yana mai da kanshi ga abinda yake da alama dama haushin kallon da suke yake ji.

Wacce aka kira da nasmah tace ''wallahi kada ki nutsu ki gani share ki zanyi ehe idan yaso uncle Solomon din ya baki punishment ehe.'' ta fada tana miƙewa tana kashe tv bakin ta a gaba domin duk bata ji dadin abinda juniour yayi mata ba bazai ma nasreen Magana ba.?

To abinda ke gabansu suka cigaba da yi kusan minti biyar kowa na harkar gabansa, can kuma aka bude wata kofa dake can hannun dama a parloun aka fito. Bakar mata ce wacce a ƙalla zata kai kimanin shekaru 32 ,amma hutu da tsafta ya ɓoye baƙi da shekaru da take dauke dasu, sanye take da jar atamfa mai ratsin ruwan omo riga da zani sai dankwali kalan atamfar daure bisa kanta sanye take da takalmi shina kalar ruwan omon hannun ta rike da wani littafi Mai kama da kundi,cikin takun ta na kasaita take takowa har ta iso falon, duk hankalin su ya koma gare ta, cikin Muryar ta mai amo da dadi tace ''hayaniyar mai kuke."

Cikin nuna alamun shima bai ji dadi ba ''yace ammi nasmah ce mana, way zata koyawa nasreen home work sai ta kunna kallo kinsan nasreen da tv to taki maida hankali kuma shine take kawo min kararta ,na sata ta kashe tv.'' Ya faɗa yana maida hankalinsa ga abinda yake.

''Baki ji nasmah nace inday lokacin karatu ne ban yarda a kunna tv ba da yake ba'a fada miki ki ji saida kika kunna wa zaki wa complain banison irin haka kina ji ko?'' matar ta tanbaya wacce da alama mahaifiyar su ce dan babu wani maraba da yara matan kamar an tsaga kara kamar su daya sai da namijin ne suka banbanta.

Naji ammi cewar nasmah tana maida hankalin ta ga text book din.

Kiran sallar magriba ita ta tashe su suna kokarin shiga alwala aka turo kofar falon aka shigo.  Farin maguidanci wanda a ƙalla zaiyyi shekaru 40 a Duniya fari sol mai yalwan gashin jiki, kansa a cike da gashi haka nan fiskar sa wacce tasha gyara sanye yakee da shadda ruwan sararin samaniya dogo ne SOSAI mai dogon hanci fuskar sa dauke da murmushi yake fadin ''afuwan Wallahi aiki yayi min yawa a asibiti shiyasa dafatan ba'a yi fushi ba dani?"

Duka wajen shi suka yi wo inda yaron ya karbi jakar dake hannun sa, kamar su daya da yaron kamar yayi kaki ya tofar,''sannu da zuwa Abba'' dukkansu suka faɗa a tare. Sannan mahaifiyar su tace Barka da dawowa Abba.

Murmushi yayi mai tafiya da rai da ruhi sannan yace ''Nagode ammi'' itama dariyar tayi sannan tace ''aje ayi alwala ko?" Da to suka amsa sannan kowa ya nufi inda zaiyyi alwalar.

"Barka da dawowa farin ciki na'' matar ta faɗa tana murmushi mai kayatarwa. "Barka day duniya ta dafatan komai lafiya? ''lafiya alhamdulillah sai kewar ka tare da zumuɗi sake ganin ka kuma Allah ya dawo mana da kai lafiya.'' ''masha Allah mungode Allah bari muje masallaci ake ayi salla'' ya faɗa yana wuce wa cikin falon.

Alwala suka yi gaba daya mazan suka wuce Masallaci su kuma matan suka tada nasu a gida. Baya an isar da isha suka shigo gida a jere gwanin sha'awa uba da ɗa suna taɗin su suka iso falon, a zaune suka same su kan kujera suma sun idar da tasu sallar dan haka suka dunguma suka wuce dining.

Bayan gana cin abinci suka dawo parlou suka zube inda hira ta barke kowa yana fadin albarkacin bakinsa, banda nasmah dake zaune ko kallo basu ishe ta ba, kowa yana fadin abinda yake so ko ya faru a makaranta banda ita da take kwance ta lumshe ido kawai.

Cikin mamakin irin miskilanci na nasmah da ya zame mata jiki tace ''yanzu ke haka zaki cigaba da rayuwa kenan na rasa meke damunki bakin hali ne ko kuwa zallar iskanci ne? Cikin yan uwanki ana tafi bazaki saka baki ba sai dau ki tsume ki kwanta bazaki ce komai ba? Allah ya shirya ki wallahi ya sa ki gane. Mahaifiyar yaran tayi maganar alamar abin na mata ciwo.

''to dan Allah ammi me matsalarki haka nan fa take ko ki barta mana duk ba ke ta gado ba?" Mahaifin nasu ya faɗa yana kashe mata ido alamar wasa .

"Ni wallahi ba haka nake ba nasmah ta iya bakin hali da kake ganin ta ba zaka zauna kayi dariya a tsakanin yan uwanka ba sai miskilanci da tarin wawta? ''maganar ya isa haka nan ammi a barta mamana taji fadan kuma zata gyara pls! ''wallahi nasmah Bata yi halin anty ba anty mai son mutane da faran faran amma NASMAH sai tsumewa da kuntume wa abinda ta iya kenan Allah ya kyauta! Ameen duka suka amsa sannan suka cigaba da taɗin rayuwa. 

Kamar kowanne rana karfe tara da rabi kowa hake wucewa wajen baccin sa dan haka kowa ya mike, juniour ya wuce wani kofa dake hannun dama a parloun kusa da kofar da matar ta fito su kuma matan suka wuce suma nasu dakin mai dan karamin kofa, ''ayi addu'ar bacci'' cewar mahaifiyar su tana binsu da kallo.

 Taɗi suka cigaba dayi a kan Ayyukan su. wajen goma saura na dare saƙo ya shigo wayar ta, a ranta ta raya ''sakon da kullum nake bacci dashi nake farka wa dashi ya zama min jiki'' ɗan gyara zama tayi sannan ta jawo wayar mijin na kallon ta bai ce komai ba. A hankali ta fara karanta sakon can gaya ta zaro ido kamar zasu faɗo. Da sauri ya taso ya iso gareta yana ''fadin lafiya kuwa?''

''sakon nuwairah yasha banban da na kowanne lokaci yasha banban da na kowanne rana lallai nuwairah ta fara wuce gona da iri.'' ta fada tana miƙa masa wayar.

_tabbas kina kokari barrister Amma zan dawo gare ku nan ba da jimawa ba ki shirya karɓar nuwairah dan da ta fito sunanki da ke da ahalinki matattu,ki gaya wa wannan tsohuwar alkalin ta sassauta yanke wa mutane hukunci haka nan domin nata hukuncin yana nan zuwa, yar halak nuwairah._

Abinda ke cikin sakon kenan. Share gumin da ya zubo masa a gefen fuska yayi sannan yace ''lallai nuwairah ta fara wuce gona da iri abin ya bar kai na yabar kanki ya koma kan anty kuma? Inday haka ne na shirya karbar nuwairah ta kowanne irin fuska, zan tunkare ta muyi gaba da gaba da ita watakila zata tabbatar karfin HUDAY da nata ba daya bane. Yana maganar ne yana raba idon shi kowanne lungu da sako dake parloun kamar wanda zai hangi ita nuwairahn anan.

Cikin kwantar da hankali matar tace ''nuwairah tayi kaɗan ta daga maka hankali doctor, duk da kuwa nasan tayi riƙar da Allah ne kawai zai iya fidda mu daga sharrin ta kar ka manta mun rike Allah dashi kuma muka dogara babu wani abinda zai same mu Wanda baya rubuce cikin littafin ƙaddarar mu mu rike Allah sai komai ya tafi mana kamar shan ruwa ma'ana cikin sauki kenan, mu kanmu munfi karfin nuwairah balle anty duk yadda take tunanin kaiwa a tsageranci akwai wanda suka dama ta kuma sanye a iskanci dan haka nuwairah bata taɓa daga min hankali ba bana saka ta cikin abinda zai dame ni kwantar da hankalinka zamuyi maganin komai kuma cikin sauki da yardar Allah.''

''Ina fatar haka insha Allah yarinyar hatsabibiya ce duk yanda Ni zan kwatanta miki halin nuwairah bazaki gane ba duk da ban san munanan halayen ta ba kamar yanda ANWAR ya sani amma tabbas zan gaya miki wasu daga ciki, tunda Ni har zaman aure nayi da ita. Ya faɗa fuskar shi da alamar damuwa.

Maganar ta dake ta amma ganin yanda fiskar shi ta canza Duk ya shiga damuwa ya saka ta danne nata damuwar ta shiga kwantar masa da hankali.

Washe gari tun asuba ta farka ana kiran salla HUDAY da juniour suka wuce masallaci, ita kuma ta tashi nasmah da NASREEN suka yi salla sannan suka fara shirin makaranta. Sai da gari yayi shaa sannan suka shigo a gurguje juniour ya shiga shiri domin ya kusa makara, kullum haka suke sai gari yayi haske suke shigowa gida. Kamar kullum sun gana shiri tsaf cikin uniform din su na makaranta wanda yaji guga kamar sabo, matan sanye da riga mai dogon hannu yar ciki sai kuma wata kamar doguwar riga a kayi ita kuma mai hannun vase sai farin hijab akan nasmah ita kuma nasreen hula mai kalan uniform din, shi kuma juniour riga ce da kuma necktied sai bakin takalmi da kuma hula, sunyi kyau matuka sai kyallau da kamshin turare suke haka suka fito, kamar kullum idan mahaifin su zai je asibiti shi take ajiye su ya wuce idan kuma bazai je asibiti da wuri ba sai drivern su wanda police be shi yake ajiye su sai ya koma ya dauko su, a nutsuosuka fito cikin takunsu irin na ya'yan masu hali wanda kudi yayi wa jagab suka tsaya a bakin motar, mahaifiyar su da ta rakosu tace ''allah ya kiyaye ayi karatu lpya a maida hankali. '' to ammi duka suka amsa sannan suka shiga drivern ya ja motar aka bude masa wakeken gate din ya fice.

A hankali ta sauke ajiyar zuciya tana juyawa suka ci karo, murmushi ta sake a hankali tana kallon shi, cikin alamun tanbaya da daga fita yace '' me kike tunani haka uhmm?'' ''wallahi hankali na ya kasa kwanciya game da yaran nan haka kawai nake jin kamar wani mummunan abu zai kasance dasu duk da nasan Allah baya daurawa bawa abinda bazai iya ba amma tabbas zan shiga wani hali idan laifi na ko naka ya shafi su nasmah zan shiga matukar damuwa, musamman nasmah a zahiri itace halin ta ya banban ta amma tabbas yarinyaar tana da wata irin fikira da kuma nuna halin ko ina kula ga mutane tabbas akwai haɗaka tattare da ita tana da sanyin hali, gaba daya idan zasu tafi makarantar nan har suke har su dawo hankali na baya kwanciya sai na gansu cikin gida ko kadan bana jin daɗi wallahi.''

''karki damu JANNAT Insha Allahu babu abinda zamu ji mu gani sai alkairi babu kuma abinda zai faru da yardar Allah ya'yan mu suna tafe ne da addu'ar iyaye a tattare dasu ki kwantar da hankalinki kinji? Banison ki ringa saka damuwa irin wannan a ranki. ''Tabbas dole na damu amma Insha Allah babu ma abinda zai faru sai alkairi.'' ''yawwa cutie haka nake son kice Allah ya rufa mana asiri.'' da ameen ta amsa sannan suka shiga gida.

Suna zama kiran waya ya shigo da murmushi a fuskarta ta dauka tana fadin ''anty ce'' shima murmushi yayi yace dauki. Cikin azama ta dauka kamar dama jira take ayi kiran ta saka a kunne tana fadin ''anty na ta kaina'' cikin dajjijuwar murya aka amsa a dayan ɓangaren da faɗin ''yata ta kaina ya gida da kowa ya yara dafatan an tashi lpya? Ya mai suna da nasreen su kadai zan tanbaya banda wannan miskilin.'' cikin dariyar ta da take ƙoƙarin danne wa tace duk suna lafiya an wuce makaranta, amma anty...'' ta karisa maganar tana shirin kwashe wa da dariya, ''nasan abinda zaki ce nasmah ce miskila ba juniour ba niday ko zaku kwana kuna faɗin hakan bazan yarda ba na gaya muku.'' sabida mai sunan ta ce ko ya za'a yi bata ganin laifin ta sai na juniour idan kaga nasmah tana tadi da wasa da dariya tabbas da anty ce amma indai da sauran mutane ne to babu ko kwatantawa ma bata yi ayi ayi tayi magana amma shiru ga fada kuma ga zuciya shiyasa ba ruwan ta da kowa.

''Ammm akan maganar case dinnan ne yasa na kira ki shin binkicen da na baki an fara aiwatar dashi kuwa? LALLAI ina son na kawo karshen case din kafin nan da wani lokaci idan son samu ne zuwa nan da wani kankanin lokaci nake son ta bayyana idan zaiyyi wu ki kokar ta kinji?'' ''ok Insha Allah anty zanyi hakan amma case din akwai damuwa sosai a cikin sa a taya mu da addu'ar samun nasara da kuma sauki wajen tafiyar da lamarin.'' ''insha Allah karki damu Allah ya taimaka'' aka fada ta cikin wayar. Ina HUDAY din''?

 ''Gashinan anty'' 

''bai fita bane''?

''Eh sai zuwa sha biyu akwia wanda zaiyyi wa surgery ne shiyasa kuma karfe 1 ne.''

''Ok tohm Allah ya bada Sa'a yasa ayi cikin nasara.''

''Ameen anty, ya abuu?''

''lafiyanshi kalau shima yanzu yake shirin fita suna da meeting da governor 10 Insha allah.''

''ok my regards to him pls anty.''

''Insha Allah zai ji.''

HUDAY dake kallon ta yace ''Wallahi kuna bani mamaki ke da anty sai ku wani manta da mutum kwata kwata idan kuna wayar nan,karfi da yaji kin kwace min uwa bata ganin kowa sai ke ko?''

Cikin dariyar ta mai sanyaya masa ruhi tace ''Ni kaina nasan na yi sa'ar uwa kuma suruka kamar anty, ita din wata halitta ce ta daban acikin mutane zuciyar ta a tsarkake take babu wani mummunan abu dake tattare da shi tabbas ka gode wa Allah da ya maka samun mahaifiya irin anty domin sunyu karanci cikin wannan duniyar tamu mai cike da ramuka da kwazazzabai, ta banbanta da kowacce irin suruka ,ita din ba irin surukan zamani bane ta dauki matar danta kamar ita ta haife ta haka nan ta dauki mazan ya'yan ta kamar ita ta haife su, ita anty hankali ce mai dan wani naka soyayyar anty gareni ba mai gushe wa bace ko da kuwa hankali da tunani zai bar jiki na bana jin zan iya nace hallaci da kuma alkairan anty gareni wanda har izuwa yau basu katse ba suke cigaba da gudana, son da nake wa anty shi ya shafe ka HUDAY domin anty ina jin ta kamar mahaifiya wani lokacin ma nakan iya kwatanta anty da inna ta domin inna ta haihuwa ta kawia tayi ita kuma anty itace jigo kuma matakin nasara ta, ina alfahari da samun mahaifiyar miji irin ta, sannan ina alfahari da samun miji irin ka sabida ka fito daga tsatson abinda na fi so da kauna kaf cikin duniya.

Rungumar da yayi mata ya saka ta yin shiru babu shiri.

Har abada ba zai samu mace irin JANNAT ba ALKAIRAN ta a gareshi masu yawa ne kuma mara sa yanke wa, yana addu'a kullum Allah yanda ya hada kan mahaifiyar sa da matar sa ya cigaba da hade su har tashin kiyama, sannan Allah ya cigaba da bashi Tsawon rai domin ya kyautata wa JANNAT da kuma iyayen ta da ahalin ta da kuma yan uwanta yana fatan haka insha Allah.

Karfe 11 suka fita suma domin itama tana da Shari'a karfe 1 na rana, tare suka fita ya sauke ta sannan ya wuce asibiti.

Yana isa ya wuce office dinsa ba jimawa aka turo kofar, matashi ne wanda bazai wuce shi a shekaru ba ba kuma zai gaza shi ba zasu iya zamowa dayday,sanye yake da farar shadda maroon da kuma rigan likitoci a kai. Yana shigowa yake fadin ''yanzu abdul ke gaya min ga shigo''

''shima cikin murmushi yake fadin wallahi yanzu nan shigowa na wannan patient din da za'a yiwa surgery ne zamu shiga anjima kadan shiyasa ban fito ba da wuri.''

''Eyya masha Allah, yasu juniour? Ina my queen? Ya faɗa yana dariya.

Lafiya ƙalau alhamdulillah duk suna skull  ishaq ya sauke su tun dazu ya su Sarkin rawan kai? Ya faɗa yana dariya.

''Ban sani ba malam mata da mijin ta da komai ka ringa gaya mata mai tawan kai wallahi kada ka kiyaye Ni Allah kuwa ranka zai ɓaci idan ka sake cewa matata mai rawan kai, ya faɗa da alamar baya son sunan da HUDAY din ya fada.

Haka suka cigaba da wasan su na barkwanci har lokacin shigar shi ayki yayi dan haka ya wuce yabar ANWAR din a office Yana shan coffee da tsakar rana domin shi mayen cofee ne.

Karfe 2 ta shigo gida a gurguje take shirin daura girki dan bata don yara su dawo daga makaranta basu samu abinci ba da yake 4 ake taso su, tana shigowa ta fada kicin ta shiga kicin kicin daure girki.

*********

Tunda jirgi ya sauke su a filin sauka da tashin jirage dake lawanti. Take harba ido domin rabon ta da garin tsawon wata uku kenan shima da ta shigo bata dade ba ta koma, a hankali take saukowa daga matakalar benen ,sanye take da yellow wando da kuma riga mai ruwan golden Wanda suka bi jikinta suka zauna cif tana da diri sosia kuma fara ce kal ba sirirya bace sosai amma bata da ƙiba a tsume take fuskar ta kumshe da gilashi da mamaye duka rabin fuskar, karamar jaka ce a hannun ta( hand bag)sai dayan kuma karamar trolley kanta yane da karamin mayafi, bakin ta yana taunar cingam., Tana gama saukowa daga jirgin ta ajiye trolleyn ta bude karamar jikar ta dauko wayar ta samfurin iPhone 11 pro, Kira tayi ana dauka tace '' Use where are you? Gani a lawanti pls kazo ka ɗauke yanzu isowa ta kasar jiya na duro daga Amirka na tsya a Abuja ina da appointment da wani Senator yanzu isowa ta Gombe kazo ka ɗauke ni. Tana faɗin haka ta kashe kiran.

Sabon layi ta ciro cikin jaka sannan ta daura a wayar ta shiga rubutu kamar haka

_Zan bayyana a Lokacin da bazaku iya tare Ni ba tabbas zan dau fansa kuma fansa mai muni, wait for me, nuwairah_

Abinda ta rubuta kenan cikin wayar ta tura, sannan ta  cire sim din ta karya ta cigaba da taunar cingam dinta. A hankali ta furta ''yanzu ma aka fara.''✍️



Kana buƙatar tsira?🏃‍♀️

To kiyaye salla a kan lokutan su🕕




Kafcen ba a haka zai tsaya ba kamar yanda kuka gani a sama zaku ga wani note basai na gaya maku na menene ba wacce ta karanta ta sani, to haka littafin zai cigaba da zuwa muku da abubuwa irin na gyaran jiki da kuma gyara aure da gyara sanwa da kuma gyara muhalli gyaran Addini yanda mutum zai kyautata tsarkin sa da kuma kyautata ibadar sa duk a cikin wannan littafi na JANNAT (tsugunno bata kare ba)


Littafin JANNAT littafin kudi ne game buƙatar karanta wannan littafin daga farko har karshe zata biya kudin ta Naira dari biyu cas ta wannan account din 0009243783 Nafisa Rabiu Umar jaiz bank, sai a turo shaidar biya ma'ana Screenshot KENAN ta wannan lambar 07059305867 ko katin waya na MTN ta wannan lambar 07059305867 hoton katin za'a turo, free PAGES zasu kare ne da nayi page ashirin cif insha Allah. Na fada JANNAT (tsugunno bata kare ba) na kudi ne kar wata ta gaya min maganar wofi idan na gama free PAGES Dan bazan dauka ba a kiyaye. Mai bukatar biya zai iya biya tun daga yanzu domin wanda suka shirya har na fara jin alert, idan na gama free PAGES bazan tsaya ba zan cigaba ne da posting kawai.


#share 

#comment

#Vote

Pls 

Dan girman Allah duk wacce ta karanta tayi share sabida Allah



*MRS ABDULL CE*✍️

Post a Comment

ADS HERE
ADS HERE